Tuesday, December 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ji irin Wulakancin da Akawa Ganduje kamin ya sauka daga shugaban APC

Ji irin Wulakancin da Akawa Ganduje kamin ya sauka daga shugaban APC

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbata cewa Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga shugaban APC. Wasu bayanai sun ce kamin saukarsa Ganduje, an cire duk wasu kayan aikinsa daga ofishinsa dake hedikwatar jam'iyyar APC dake Abuja. Rahoton yace kuma daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu aka umarci Ganduje ya sauka daga mukamin nasa. Wane ne Abdullahi Ganduje? An haifi Abdullahi Umar a ƙauyen Ganduje da ke cikin ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ta jihar Kano a 1949. Ya fara karatun Ƙur'ani da Islamiyya a ƙauyensu, inda ya samu ilimin addini. Ya shiga firamare ta Dawakin Tofa daga 1956 zuwa 1963. Ganduje ya fara makarantar sakandiren Birnin Kudu a 1964 inda ya kammala a 1968. Ya shiga makarantar horar da malamai da ke Kano tsakanin 1969 zuwa 1972. Tsohon gwamnan jihar Kanon ya samu d...
Ji bayani dalla-dalla: Shugaba Tinubu ne yacewa Ganduje ya sauka daga shugabancin APC

Ji bayani dalla-dalla: Shugaba Tinubu ne yacewa Ganduje ya sauka daga shugabancin APC

Duk Labarai
Shugaban jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga muƙaminsa bayan kwashe ƙasa da shekara biyu yana jagorancin jam'iyyar. Wasu majiyoyi daga fadar shugaban Najeriya sun tabbatar wa BBC cewa Ganduje ya ajiye muƙamin ne bayan da fadar shugaban ƙasa ta umarce shi da yin hakan. "Da gaske ne Ganduje ya sauka tun jiya (Alhamis) aka ba shi umarnin ya rubuta takardar murabus, a yau da safe (juma'a) ya miƙa takardar," in ji majiyar. Hakan na zuwa ne bayan wani rudani da aka samu kimanin mako ɗaya da ya gabata a lokacin taron jam'iyyar ta APC na arewa maso gabashin ƙasar. A lokacin taron, wasu daga cikin ƴan jam'iyyar sun nuna fushi kan rashin bayyana sunan mataimakin shugaban ƙasar Kashim Shettima a matsayin wanda zai mara wa Tinubu baya takarar shugab...
Da Duminsa: A karshe dai Shugaban jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga mukaminsa

Da Duminsa: A karshe dai Shugaban jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga mukaminsa

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbata cewa, shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga mukaminsa. Jaridar Vanguard ta bayyana cewa ta samu tabbacin saukar Ganduje daga mukaminsa. Babu tabbacin dalilin da yasa Ganduje ya sauka daga mukaminsa amma wata majiya daga jam'iyyar ta tabbatar da saukar Ganduje. Rahotanni sun ce kamin saukarsa daga mukamin, an dauke duka wasu abubuwan sa daga ofishin shugaban jam'iyyar dake Abuja.
DA DUMI-DUMI: Ganduje na shirin sauka daga shugabancin jam’iyyar APC na ƙasa

DA DUMI-DUMI: Ganduje na shirin sauka daga shugabancin jam’iyyar APC na ƙasa

Duk Labarai
Daga yanzu zuwa kowanne lokaci, Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Ganduje, zai mika takardar murabus dinsa, in dai ba canja ra'ayi ya yi ba. Majiyoyi sun shaidawa DAILY NIGERIAN cewa za a maye gurbin Ganduje da Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na ƙasa na yanzu har zuwa lokacin babban taron jam’iyyar da za a yi a watan Disamba. Rahotanni sun nuna cewa wannan mataki na murabus na da nufin shawo kan korafe-korafe daga jiga-jigan jam’iyyar daga yankin Arewa ta Tsakiya, da kuma ƙara karfin tasirin muryar adawa daga cikin jam’iyyar da ke ƙara ta’azzara. Idan za a iya tunawa an nada Ganduje a watan Agusta 2023 bayan murabus din Abdullahi Adamu daga wannan mukami. Tun daga lokacin, jiga-jigan siyasa daga Arewa ta Tsakiya suna ci gaba da neman a mayar da kujerar shugabancin jam’iyy...
Da Duminsa: Shugaba Tinubu zai mayar da Gwamna Fubara kan mukaminsa na Gwamnan jihar Rivers, ji sharudan ban mamaki da aka gindaya masa

Da Duminsa: Shugaba Tinubu zai mayar da Gwamna Fubara kan mukaminsa na Gwamnan jihar Rivers, ji sharudan ban mamaki da aka gindaya masa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai mayar da Gwamna Simi Fubara na jihar Rivers kan mukaminsa na gwamnan jihar. Saidai an gindayawa gwamnan Sharuda kamar haka: Ba zai sake tsayawa takarar gwamnan ba a zaben shekarar 2027. Zai yadda Wike ya tsayar da 'yan takarar shuwagabannin kananan hukumomi 23 dake fadin jihar. Hakanan ya yadda ya biya 'yan majalisar jihar dakewa Wike Biyanna su 27 hakkokinsu da ya dakatar, idan ya yadda da hakan, 'yan majalisar ba zasu yi yunkurin tsigeshi ba.
Kalli yanda Wata mamakon Gobara da ba’a san daga inda ta taso ba ta barke a kasar Israyla tana ta yaduwa sosai

Kalli yanda Wata mamakon Gobara da ba’a san daga inda ta taso ba ta barke a kasar Israyla tana ta yaduwa sosai

Duk Labarai
Wata mamakon gobara ta barkena tsakiyar kasar Israyla inda take ta yaduwa sosai. Gobarar da ba'a san inda ta samo Asali ba ta tashine a birnin Ness Ziona kuma 'yan kwana-kwana na ta kokarin kasheta. Rahotanni sun ce an tattaro ma'aikatan kwana-kwana daga yankuna daban-daban dan su taimaka a kashe gobarar. Hukumomi sun ce Tuni aka fara kwashe mutane daga gidajen da Gobarar ta durfafa.
Kalli Yadda Aka Yafawa Ka’aba Sabuwar Riga Albarkacin Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1447 Bayan Hijira

Kalli Yadda Aka Yafawa Ka’aba Sabuwar Riga Albarkacin Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1447 Bayan Hijira

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Yadda Aka Yafawa Ka’aba Sabuwar Riga Albarkacin Shiga Sabuwar Shekarar Musulunci Ta 1447 Bayan Hijira.