Wednesday, December 24
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Za a fara sauya tunanin tubabbun ƴanbindigar da suka miƙa makamai a Katsina

Za a fara sauya tunanin tubabbun ƴanbindigar da suka miƙa makamai a Katsina

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ce za ta soma shirin sauya tunanin tubabbun ƴanbindigar da suka miƙa makamai nan bada jimawa ba. Gwamnatin ta ce za a buɗe azuzuwan koyar da karatu da dubarun koyar da sana'o'i domin sauya tunanin ƴanbindigar, inda daga bisani za su koma cikin al'umma. Hukumar da ke kula da ilimin manya ta jihar ce ke da alhakin tsara yadda shirin sauya tunanin tubabbun ƴanbindigar zai kasance. Ƙarƙashin shirin za a bai wa waɗanda suka miƙa makamansu damar koyon karatun zamani da na addinin musulunci tare da fahimtar da su illar kisan mutane da kuma neman fansa. Daraktar hukumar ilimin manya ta jihar Katsinan Bilkisu Muhammad Kakai, ta tabbatarwa da BBC wannan shiri da gwamnatin jihar zata fara. Daraktar ta sanar da manema labarai...
Kannywood na ta dokin Auren Malika da Abdul M. Shareef

Kannywood na ta dokin Auren Malika da Abdul M. Shareef

Duk Labarai
A yayin da ranar auren taurarin fina-finan Hausa, Abdul M. Shareef da amaryarsa, Maryam Malika ke kara matsowa, Masana'antar Kannywood sai nuna doki take. Da farko dai ganin katin gayyatar auren ne ya fara daukar hankulan mutane inda aka ga cewa ranar 27 ga watan Yuni ne za'a daura auren. Bayan nan kuma sai Hotunan kamin boki ke ta fitowa daga manyan jaruman masana'antar. Ali Nuhu na daga wadanda suka watsa hotunan bikin: MC Ibrahim Sharukhan ma ya wallafa hotunan bikin inda yake ma sabbin ma'auratan fatan Alheri: Shima Alhaji Shehe ya wallafa hotunan auren: Muna fatan Allah ya sanya Alheri ya kaimu Lafiya.
Atiku zamu zaba idan Tinubu yaki tafiya da Shettima a 2027>>Inji Mutane daga Arewa maso gabas

Atiku zamu zaba idan Tinubu yaki tafiya da Shettima a 2027>>Inji Mutane daga Arewa maso gabas

Duk Labarai
Fargaba ta kunno kai a cikin jam'iyyar APC bayan rikicin da ya faru a jihar Gombe wajan taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar daga Arewa maso gabas. Hatsaniya ta kaure a wajan taron bayan da aka bayyana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a matsayin dan takarar APC da yankin zai goyi baya amma ba'a ambaci sunan mataimakin shugaban kasar, Kashim Shettima ba. Rahotanni sun ce bayan rikicin, wasu wakilai daga jihar sun bayyana cewa, Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar zasu zaba a 2027 idan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bai tafi da Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa ba a zaben shekarar 2027. Wani daga jihar Adamawa a wajan taron ya bayyana cewa zai koma jam'iyyar PDP muddin aka cire Shettima a matsayin mataimakin shugaban kasa.
Idan baka hada kai da shugaban kasa Tinubu ba, Jihar Zamfara zata tafka Asara>>Sanata Orji Kalu ya gayawa Gwamna Lawal Dare

Idan baka hada kai da shugaban kasa Tinubu ba, Jihar Zamfara zata tafka Asara>>Sanata Orji Kalu ya gayawa Gwamna Lawal Dare

Duk Labarai
Sanata Orji Kalu ya baiwa gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare shawarar ya gyara alakarsa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana hakane a ziyarar da ya kai jihar ta Zamfara ya kaddamar da Makarantar Kimiyya da fasaha da kuma sabuwar ma'aikatar mata ta jihar Zamfara da aka gina. Sanata Kalu yace alaka me kyau da shugaban kasa, zata sa jihar Zamfara ta kara samun ayyukan ci gaba. Ya bayyana cewa, ba wai sai Gwamna Dare ya bar jam'iyyar PDP ya koma APC amma alaka me kyau tsakaninsa da shugaban kasa, zata taimaka sosai wajan ci gaban jihar ta Zamfara.
Bidiyo: Kalli Yanda ziyarar su Ali Jita da Nazir Sarkin Waka ta kasance zuwa kasar Kamaru

Bidiyo: Kalli Yanda ziyarar su Ali Jita da Nazir Sarkin Waka ta kasance zuwa kasar Kamaru

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Shahararrun Mawakan Najeriya, Nazir Ahmad Sarkin Waka da Ali Jita sun kai ziyara kasar Kamaru inda har motarsu ta makale. Ali jita ya wallafa Bidiyon yanda wannan ziyara tasu ta kasance a shafinsa na Tiktok. Lamarin dai ya dauki hankula. Kalli Bidiyon a kasa: https://www.tiktok.com/@realalijita/video/7516308497550626104?_t=ZM-8xHF92tmO1g&_r=1 Taurarin fina-finan Hausa da Mawakan Najeriya da yawane ke kai ziyara kasashen Afrika daban-daban dake yarin Hausa, irin su...
Akwai fargaba da tsoro sosai a zukatan ‘yan Najeriya saboda gazawar jami’an tsaro, da yawan ‘yan Najeriya yanzu su suke baiwa kansu tsaro>>Shugaba Tinubu

Akwai fargaba da tsoro sosai a zukatan ‘yan Najeriya saboda gazawar jami’an tsaro, da yawan ‘yan Najeriya yanzu su suke baiwa kansu tsaro>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, Matsalar tsaro da ta sha kan jami'an tsaron kasarnan ta saka fargaba da tsoro a zukatan mutane. Yace Manoma na tsoron zuwa gona, 'yan Kasuwa basu da tabbas akan tsaron rayukansu, sannan mutane an barsu da kare kansu. Shugaban ya bayyana hakane a Abuja ranar Litinin wajan tattaunawa game da gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya da canja fasalin harkar tsaron kasarnan wanda kwamitin dake kula da canja fasalin kundin tsarin mulkin Najeriya na majalisar tarayya ya shirya. Shugaban ya bayyana muhimmancin samar da 'yansandan jihohi wanda yace sune zasu taimaka sosai wajan kare kasarnan. Shugaban ya bayyana hakanne ta bakin ministan Tsaro, Mohammed Abubakar Badaru wanda ya wakilceshi a wajan taron.
Matsalar tsaron kasarnan ta fi karfin jami’an tsaron mu, ba zasu iya ba>>Shugaba Tinubu

Matsalar tsaron kasarnan ta fi karfin jami’an tsaron mu, ba zasu iya ba>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, amfanin tsarin tsaron da ake kanshi a yanzu, ya kare. Ya bayyana cewa, samar da 'yansandan jihohi yanzu ba magana bace kawai ta fatar baki ba, abune da ya zama dole dan samarwa 'yan kasa tsaro. Shugaban yace jami'an tsaron da ake dasu yanzu wanda gwamnatin tarayya ke kula dasu aiki ya musu yawa kuma basa iya samar da tsaron yanda ya kamata Shugaban yace, dolene a baiwa jihohi dama su samar da 'yansandan jihohi da zasu ira aiki ...
Karanta Jadawalin mutanen da suka rasa rayukansu a mummunan hàrìn jihar Benue

Karanta Jadawalin mutanen da suka rasa rayukansu a mummunan hàrìn jihar Benue

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wadannan jadawalin mutanen da suka rasa rayukansu ne a mummunan harin da aka kai jihar Benue wanda ya tayar da hankalin Najeriya baki daya. ADAM FAMILYTorsaar AdamDoose AdamNguyilan Adam AJAH FAMILYLydia AjahTerdoo AjahIwuese Ajah AKPEN FAMILYTerzungwe AkpenAondohemba AkpenUshana AkpenShater AkpenMercy AkpenIsaac Akpen AMAKI FAMILYFestus AmakiShater Amaki ANYA FAMILYOrbuter Anya AONDOANA FAMILYDooshima AondoanaAgbogo AondoanaErdoo Aondoana AONDOVIHI FAMILYMbakeren ...
Ba zamu yadda kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba>>Inji Kasashen G7

Ba zamu yadda kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba>>Inji Kasashen G7

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Canada inda aka yi taron kasashe 7 mafiya karfin tattalin Arziki wadanda ake kira da G7 sun bayyana cewa, ba zasu amince kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba. Kasashen sun ce suna son a samu zaman lafiya a gabas ta tsakiya kuma sun amince kasar Israyla na da damar kare kanta. Sun bayyana cewa kasar Iran itace ummul aba isin rashin zaman lafiyar da ake fama dashi a yankin na gabas ta tsakiya. Dan haka suna jaddada matsayarsu ta cewa ba zasu amince kasar Iran ta mallaki makamin kare dangi ba. Kasashen G7 da shuwagabannin su sune kamar haka: Donald J Trump (The USA)Keir Starmer (The UK)Friedrich Merz (German Chancellor)Giorgia Meloni (Italy PM)Emmanuel Macron (France)Shigeru Ishiba (Japan PM) Wasu kasashen Duniya da aka gayyata zuwa wannan taro su...