Ji yanda wata mata ta kàshè kishiyarta a Garin Daura na jihar Katsina
Ƴan sanda a jihar Katsina sun kama wata matar aure da ake zargi da kashe kishiyarta.
Lamarin ya faru ne a bayan wata makarantar firamare ta Dadi da ke unguwar Sabon Gari, a ƙaramar hukumar Daura bayan da wata matsala ta cikin gida tsakanin matan auren biyu ta rikiɗe zuwa rikici mai muni da ya kai ga mutuwa.
Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Abubakar Sadiq, ya fitar a ranar Lahadi, inda ya bayyanawa manema labarai abin da ya faru.
Sanarwar ta ce: “A ranar 24 ga Mayu, 2025, da misalin ƙarfe 11 na dare ne ofishin ‘yan sanda na Sabon Gari suka samu rahoto daga wani Nasir Yusuf, mijin matar, cewa ya dawo gida daga kasuwa ya tarar da matarsa ta farko mai suna Zainab Lawal tana kwance cikin jini, an caka mata wuƙa sau da dama.”
“Da sa...








