Saturday, March 21
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Hukumar alhazan Najeriya ta saka ranar fara kai maniyyata Saudiyya

Hukumar alhazan Najeriya ta saka ranar fara kai maniyyata Saudiyya

Duk Labarai
Hukumar Alhazai ta Ƙasa a Najeriya ta sanar da kammala shirye-shirye domin soma jigilar maniyyata aikin Hajjin bana zuwa kasar Saudiyya ranar 9 ga watan Mayu. Hukumar ta Nahcon ta sanar da hakan ne bayan wata ganawa da shugabanta da wakilan majalisar gudanarwa suka yi da Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima. Mataimakin shugaban kasar ne ya gayyaci shugaban hukumar Farfesa Abdullah Saleh Usman da wakilan sashen gudanarwa zuwa ganawar a ofishinsa domin sanar da shi inda aka kwana game da shirye-shiryen aikin hajjin. "Mun yi masa bayani game da shirye-shiryenmu a Makkah da Madina da Arafa kuma ya gamsu, har ma ya ba mu umarnin yadda za mu haɗa kanmu mu yi aikin har zuwa ƙarshensa," kamar yadda Farfesa Saleh ya shaida wa BBC. Kazalika, shugaban ya ce suna sa ran kammala aikin k...
Kotu a Kano ta yankewa Matashi hukuncin kìsà saboda kàshè mata da miji da diyarsu

Kotu a Kano ta yankewa Matashi hukuncin kìsà saboda kàshè mata da miji da diyarsu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Babbar Kotu a jihar Kano ta yankewa Salisu Idris mazaunin Unguwar Gayawa hukuncin kisa ta hanyar rataya. Mai Shari'a Amina Adamu Aliyu ta yanke hukuncin a kashe Salisu ta hanyar rataya sakamakon bankawa wata mata da mijinta tare da ɗansu ɗan shekara 2 wuta da yayi sanadiyar mutuwarsu. Al'amarin ya faru tun a shekarar 25 ga September, 2019 a unguwar Gayawa dake ƙaramar hukumar Ungoggo, a jihar Kano da misalin ƙarfe 2:00 na daren wannan rana. Mukhtar Abdullahi Shuaibu Fassara a ...
Dansandan Najeriya ya Harbi Kansa Da Bìndìgà ya mùtù

Dansandan Najeriya ya Harbi Kansa Da Bìndìgà ya mùtù

Duk Labarai
Dansandan Najeriya me suna Maxwell Zabu ya Harbi Kansa inda ya mutu har Lahira. Dansandan na aikin baiwa tsohon shugaban karamar hukumar Fatakwal ta jihar Rivers, Victor Ihunwo kariyane inda a ranar Talata ta harbi kansa ya mutu. Lamarin ya farune a Eagle Island gidan tsohon shugaban karamar hukumar. Kakakin 'yansandan jihar, Grace Iringe-Koko ta tabbatar da faruwar lamarin inda tace suna kan bincike.
YANZU-YANZU: Gwamna Bago Ya Sanya Dokar Ta Baci A Garin Minna Biyo Bayan Rikìçe-Ŕikicen Ta Ta’ďdançi

YANZU-YANZU: Gwamna Bago Ya Sanya Dokar Ta Baci A Garin Minna Biyo Bayan Rikìçe-Ŕikicen Ta Ta’ďdançi

Duk Labarai
Gwamnan jihar Neja, Umaru Mohammed Bago, ya sanya dokar taƙaita zairga-zirgar baburan haya daga karfe 6 na yamma zuwa 6 na safe a Minna babban birnin jihar sakamakon yawaitar rikicin 'yan daba a birnin. A cewar gwamnan, yanzu haka an takaita zirga-zirgar 'yan acaɓa da babura masu ƙafa uku a wannan tsakanin. Bago ya bayyana hakan ne yayin wani muhimmin taron tsaro da masu ruwa da tsaki suka yi da sarakunan gargajiya da shugabannin hukumomin tsaro a gidan gwamnati yau Talata. ''Babu wanda zai sake ɗaukar kowane irin nau'i makami a garin Minna. Ina bai wa jami'an tsaro umarni, duk mutumin da kuka gani da makami ku ɗauke shi a matsayin ɗanfashi da makami.'' in ji shi. Ya bayyana cewa sabon matakin na da nufin daƙile matsalolin tsaro da ke ƙara taɓarɓarewa a babban birnin jihar. ...
An yankewa matashi hukuncin kìsà saboda kàshè Kishiyar mahaifiyarsa me dauke da juna biyu da diyarta a Kano

An yankewa matashi hukuncin kìsà saboda kàshè Kishiyar mahaifiyarsa me dauke da juna biyu da diyarta a Kano

Duk Labarai
Babbar kotu a jihar Kano ta yankewa matashi me suna Sagir Rijiyar-Zaki dan kimanin shekaru 22 hukuncin kisa bayan samunsa da laifin kashe kishiyar mahaifiyarsa da diyarta. Sagir ya yi amfani da sukundireba ya cakawa kishiyar mahaifiyarsa me suna Rabiatu Sagir me kimanin shekaru 25 sannan ya shage diyarta, Munawwara me shekaru 8 itama ta mutu. A ranar April 22, 2025 ne Mai shari'a Amina Adamu-Aliyu ya ce an gabatar da gamsassun shaidu da suka tabbatar wanda ake zargi yayi kisan. Dan haka ya yankewa wanda ake zargin hukuncin kisa ta hanyar Rataya.
Wani abu me kama da Bam ya fashe a Kaduna, Mutane 2 sun mutu, 3 sun jikkata

Wani abu me kama da Bam ya fashe a Kaduna, Mutane 2 sun mutu, 3 sun jikkata

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wani abu me kama da bam ya fashe a unguwar Abakpa dake kusa da tsohuwar NDA a cikin garin Kaduna. Abin yayi sanadiyyar mutuwar yara biyu,daya sunansa Imam me shekaru 13 dayan kuma Narin me shekaru 6. Lamarin ya farune a ranar Talata, 22 ga watan Afrilu. Tuni jami'an tsaro suka kai dauki wajan. Zuwa yanzu dai ba'a tabbatar da meme ya fashe ba. Wani shaida yace yana cikin wanda ya ji fashewar abin inda ya fito dag ya ga meme sai ya ga Imam ya jikkata, yace kamin su kaishi Asibiti ya rasu. Hakanan lamarin yayi sanadiyyar jikkatar mutane 3.
ABIN A YABA: Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja

ABIN A YABA: Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Malama Hajara Kenan Wacce Ta Gina Katafaren Sabon Masallaci A Unguwar Ndeshi Dake Karamar Hukumar Mokwa A Jihar Neja Wace fata za ku yi mata?
‘Yan Bìndìgà sun sakawa mutanen jihar Zamfara harajin Naira Miliyan 60 saboda sun baiwa sojoji bayanan sirri aka kai musu samame

‘Yan Bìndìgà sun sakawa mutanen jihar Zamfara harajin Naira Miliyan 60 saboda sun baiwa sojoji bayanan sirri aka kai musu samame

Duk Labarai
'Yan Bindiga a jihar Zamfara sun kakabawa kauyuka 12 harajin Naira Miliyan 60 saboda sunce mutanen wadannan kauyukan sun baiwa jami'an tsaro bayanan sirri da suka kai ga kai musu hari da tarwatsa su. Garuruwan da 'yan Bindigar suka sakawa wannan harajin sun hada da Koloma, Dan Hayin Zargado, Zargado, Dan Godabe, Sabuwar Tunga, Makini, Bubaka, Yelwa, Bahwada, Koda, Manya, da Kabusu. Mutanen kauyen sun bayyana cewa idan suka sake basu biya wannan haraji ba, 'yan Bindigar zasu afka musu da kisa da garkuwa da kona musu gidaje. Bakatsine ne ya bayyana hakan a shafinsa na X inda yace idan ba'a dauki mataki ba, komai na iya faruwa. Tsohon Kansilan Dankurmi, Hon. Iliyasu Salisu Dankurmi ma ya tabbatar da hakan a hirar da BBChausa ta yi dashi.