Ba zamu saurareki ba, Majalisar Dattijai ta yi watsi da korafin Sanata Natasha Akpoti akan Sanata Godswill Akpabio na zargin ya nemeta da lalata
Kwamitin da'a na majalisar Dattijai yayi watsi da korafin da Sanata Natasha Akpoti ta shigar gabansa inda take zargin cewa, kakakin majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya nemeta da lalata.
Sanata Natasha Akpoti a zaman majalisar a jiya, Laraba ta gabatar da korafi a hukumance gaban majalisar inda kakakin majalisar Godswill Akpabio wanda shine take zargi da neman yin lalata da ita yace mata ta mika takardar korafin inda a karshe yace a kai takardar gaban kwamitin da'a na majalisar.
Saidai a zaman Kwamitin da'a na majalisar, shugaban Kwamitin, Sanata Neda Imasuen ya bayyana cewa ba zasu saurari korafin na Sanata Natasha Akpoti ba saboda maganar na kotu.
Yace a dokar majalisa, duk maganar dake kotu, kwamtinsu ba zai tattaunata ba.
Saidai kamin a tashi daga zaman majalisar, Sanata ...








