Sunday, February 22
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ba zamu saurareki ba, Majalisar Dattijai ta yi watsi da korafin Sanata Natasha Akpoti akan Sanata Godswill Akpabio  na zargin ya nemeta da lalata

Ba zamu saurareki ba, Majalisar Dattijai ta yi watsi da korafin Sanata Natasha Akpoti akan Sanata Godswill Akpabio na zargin ya nemeta da lalata

Duk Labarai
Kwamitin da'a na majalisar Dattijai yayi watsi da korafin da Sanata Natasha Akpoti ta shigar gabansa inda take zargin cewa, kakakin majalisar, Sanata Godswill Akpabio ya nemeta da lalata. Sanata Natasha Akpoti a zaman majalisar a jiya, Laraba ta gabatar da korafi a hukumance gaban majalisar inda kakakin majalisar Godswill Akpabio wanda shine take zargi da neman yin lalata da ita yace mata ta mika takardar korafin inda a karshe yace a kai takardar gaban kwamitin da'a na majalisar. Saidai a zaman Kwamitin da'a na majalisar, shugaban Kwamitin, Sanata Neda Imasuen ya bayyana cewa ba zasu saurari korafin na Sanata Natasha Akpoti ba saboda maganar na kotu. Yace a dokar majalisa, duk maganar dake kotu, kwamtinsu ba zai tattaunata ba. Saidai kamin a tashi daga zaman majalisar, Sanata ...
Kalli Bidiyon yanda Sanata Natasha Akpoti ta kunyata kakakin majalisar dattijai Sanata Godswill Akpabio a yayin zaman majalisar a yau, Laraba

Kalli Bidiyon yanda Sanata Natasha Akpoti ta kunyata kakakin majalisar dattijai Sanata Godswill Akpabio a yayin zaman majalisar a yau, Laraba

Duk Labarai
A yau a hukumance, Sanata Natasha Akpoti ta kunyata kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio inda ana zaune a majalisar ta tashi tsaye ta gabatar da korafinta na cewa ya nemi yin lalata da ita. Tace tana gabatar da korafin take mata hakkinta da neman yin lalata da ita da kakakin majalisar yayi. Tace idan za'a iya tunawa a Gidan talabijin na Arise TV ta yi wannan zargi. Tace to yau gashi ta kawo a hukumance tana zargin kakakin majalisar. Bayan ta gama jawabinta, ta nemi kakakin majalisar ya bata umarnin gabatar masa da takardar zargin, inda yace ya bata umarni. Haka ta taka tinkis-tinkis ta je gaban sandar majalisar ta rusuna sannan ta ajiye takardar korafin a gaban kakakin majalisar. Ya bayar da umarnin a mikawa kwamitin ladaftarwa na majalisar da takardar korafin...
Ƴansanda sun kama wata mata bisa zargin kàshè kishiyarta a Bauchi, bayan ta kkàsheta, ta kuma watsa mata ruwan zafi sannan ta tattara buhu ta cinnawa gawar wuta

Ƴansanda sun kama wata mata bisa zargin kàshè kishiyarta a Bauchi, bayan ta kkàsheta, ta kuma watsa mata ruwan zafi sannan ta tattara buhu ta cinnawa gawar wuta

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan Najeriya reshen jihar Bauchi ta ce ta kama wata mata mai suna Fatima Mohammed kan zargin kashe kishiyar mai suna Hajara Isa hanyar shaƙeta a gidan mijinsu. Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, Ahmed Wakil ya fitar ranar Talata ya ce tuni rundunarsu ta ƙaddamar da bincike kan lamarin. Ya ce mijin matan - Sale Isa - ne ya kai ƙorafi wajen ƴansanda a ranar Talata. Wakil ya ce bayan fara gudanar da bincike ƴansanda suka kama matar mai suna Fatima Mohammed mai shekara 28, wadda daga baya ta amsa laifinta a lokacin ƴansanda suke tuhumarta. “A lokacin da ake tuhumarta ta amsa laifinta inda tace shaƙe kishiyartata ta yi, har sai da ta mutu'', in ji sanarwar. Sanarwar ta ƙara da cewa ''bayan ta kashe ta, ta yi ƙoƙarin yin ɓadda-bami, ta yadda ba ...
Karya Sanata Natasha take min mamana ta min tarbiyya me kyau, bana cin zarafin mata>>Sanata Godswill Akpabio

Karya Sanata Natasha take min mamana ta min tarbiyya me kyau, bana cin zarafin mata>>Sanata Godswill Akpabio

Duk Labarai
Sanata Godswill Akpabio kakakin majalisar dattijai ya bayyana cewa, Karya sanata Natasha Akpoti ke masa da tace ya nemi yin lalata da ita. Ya bayyana hakane a zaman majalisar na ranar laraba. Inda yace shi bai taba cin zarafin kowace mace ba a rayuwarsa ya kara da cewa shi har kyautar girmamawa aka bashi saboda kare hakkin mata. Sanata Natasha Akpoti dai ta zargi kakakin majalisar dattijan da neman yin lalata da ita shiyasa baya bata damar gabatar da ayyukan ci gaba a majalisar.
Motar ‘yansanda ta kashe karamar yarinya a wajan bin me laifi

Motar ‘yansanda ta kashe karamar yarinya a wajan bin me laifi

Duk Labarai
Motar 'yansanda a jihar Legas ta kashe wata karamar yarinya me shekaru 6 a yayin da suke bin wani me laifi. Lamarin ya farune a yankin Iyana Ipa dake birnin Legas. Mahaifin yarinyar, Nnamdi Ugorji ya bayyanawa majiyarmu cewa, 'yansanda daga ofishin 'yansandan na Mosholashi ne suka biyo me laifi inda a haka ne suka buge diyarsa me shekaru 6 ta mutu. Yace diyarsa da 'yan uwanta sun je banki ne ciro kudi a kan hanyar ne motar 'yansandan ta bugesu, yace kuma 'yansandan sun so canjawa lamarin fasali inda suke nuna cewa motarsu ta yi kulikulin kuburane. Yayi kira ga shugaban 'yansanda da shugaban kasa da ministar mata da su tabbatar wanda suka aikata wannan lamari an hukuntasu.
Kalli bidiyon yanda Sheikh Pantami ya fashe da kuka saboda shaukin son Annabi(SAW) yayin da yake wa’azi, lamarin ya jawo cece-kuce

Kalli bidiyon yanda Sheikh Pantami ya fashe da kuka saboda shaukin son Annabi(SAW) yayin da yake wa’azi, lamarin ya jawo cece-kuce

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Babban malamin addinin islama, kuma tsohon ministan sadarwa, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami ya fashe da kuka yayin da yake bayar da tarihin Yakun Uhud. Saidai lamarin ya jawo cece-kuce a kafafen sada zumunta. Wasu sun rikawa malam shaguben cewa da yana kan mulki rike da mukamin minista ya daina kuka inda wasu suka rika cewa yanzu da babu mukamin shine kukan nashi ya dawo. https://www.tiktok.com/@ukashabeenabdullahi/video/7478000163596832055?_t=ZM-8uQathS8...
Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Najeriya ce kasa ta 3 da ta fi yawan bashi a Afrika

Duk Labarai
Bankin (Afreximbank) ya bayyana cewa, Najeriya ce kasa ta 3 a jerin kasashen da suka fi yawan cin bashi a Africa. A wani bayani da ya fitar, bankin yace yawan ciyo bashi daga kasashen waje a tsakanin kasashen Adrica na ci gaba da karuwa. Yace hakan na faruwane saboda rashin ci gaban bangaren hada-hadar kudi na kasashen Afrikan. Bankin yace a watanni 6 na farkon shekarar 2024, kasashen Afrika 10 ne ke da kaso 69 na yawan bashin da aka ciwo a nahiyar. Kasashen sune South Africa (14%), Egypt (13%), Nigeria (8%), Morocco (6%), Mozambique (6%), Angola (5%), Kenya (4%), Ghana (4%), Côte d’Ivoire (3%), sai Senegal (3%). Bankin yace hakan na kara karuwane saboda yawan dogaron da kasashen ke yi da samun kudi ta hanyar neman tallafi daga kasashen yamma.