Sunday, February 22
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Buhari bai so Tinubu ya zama shugaban kasa ba>>Inji Dan Jarida Sam Omatseye

Buhari bai so Tinubu ya zama shugaban kasa ba>>Inji Dan Jarida Sam Omatseye

Duk Labarai
Dan Jarida, Sam Omatseye ya bayyana cewa, tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari bai so Tinubu ya zama ahugaban kasa ba. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi. Yace tun a shekarar farko aka so a samu matsala tsakanin Buhari da Tinubu amma saboda Buharin na tunanin zarcewa, shiyasa ba'a yi fadan ba. Yace cire tsohon gwamnan Edo, Adams Oshiomhole daga mukamin shugaban APC na daya daga cikin dabarun hana Bola Ahmad Tinubu zama shugaban kasa da Gwamnatin Buhari ta bijiro dasu. Yace hakanan akwai wasu gwamnoni ma da basu so Tinubu ya zama shugaban kasa ba.
Da Duminsa: Shugaban Kasar Amurka, Donald Trump na shirin soke dokar data halasta auren jinsi na ‘yan Luwadi da Magido a kasar Amurka

Da Duminsa: Shugaban Kasar Amurka, Donald Trump na shirin soke dokar data halasta auren jinsi na ‘yan Luwadi da Magido a kasar Amurka

Duk Labarai
'Yan Jam'iyyar Republican dake mulki a kasar Amurka a majalisar kasar na shirin soke dokar amincewa da auren jinsi na 'yan Luwadi da madigo a kasar. A watan Janairu ne aka fara samun wanna kira daga 'yan majalisar jihar Idaho inda suka nemi kotun kolin kasar data sake duba dokar da ta yi a shekarar 2015 data halasta auren jinsi. Bayan su, an sake samun wasu 'yan majalisar daga jihohin Michigan, Montana, North Dakota da South Dakota suma suna kiran kotun kolin data sake duba wannan hukunci nata. Dama dai tun a ranar da aka bayyana cewa, Donald Trump ne ya lashe zaben shugaban kasar Amurka aka rika samun 'yan Luwadi da madigo da yawa na kuka suna cewa sun shiga uku inda wasu suka bar kasar ta Amurka saboda sun san shugaban kasar, Donald Trump baya shiri dasu. Tuni dai shugaba Tru...
Da Duminsa: Masu Gàrkùwà da mutane sun kkàshè tsohon shugaban Hukumar shige da fici ta Najeriya

Da Duminsa: Masu Gàrkùwà da mutane sun kkàshè tsohon shugaban Hukumar shige da fici ta Najeriya

Duk Labarai
Masu garkuwa da mutane sun kashe tsohon shugaban hukumar kula da shige da fici ta Najeriya, watau Nigerian Immigration me suna David Shikfu Parradang. Rahoton theNation yace an yi garkuwa dashine a daren jiya a abuja. Ya shafe shekaru 30 yana aiki da hukumar inda yayi aiki a jihohin Kano, Lagos, Kwara, Enugu da babban birnin tarayya Abuja.
Jahilci da sakarci ne yasa Gwamnonin Arewa suka bayar da hutun Azumin watan Ramadana, idan na zama shugaban kasa ba zan yadda da wannan ba>>Sowore

Jahilci da sakarci ne yasa Gwamnonin Arewa suka bayar da hutun Azumin watan Ramadana, idan na zama shugaban kasa ba zan yadda da wannan ba>>Sowore

Duk Labarai
Tsohon dan takarar shugaban kasa kuma me ikirarin fafutukar 'yancin dan Adam, Omoyele Sowore ya bayyana cewa Gwamnonin jihohin Bauchi, da Katsina, da Kano, da Kebbi da suka bayar da hutun makaranta na Azumin watan Ramadana Jahilaine kuma sakarkarune. Yace Makka da ake zuwa yin hajji basu kulle makarantun su saboda Azumin watan Ramadana ba wanda hakan yake nuna cewa su wadannan gwamnoni sun jahilci addinin. Yace idan ya zama shugaban kasa, ba zai bari wani gwamna yayi irin wannan abin ba. Sowore ya kara da cewa, cikin makarantun da aka kulle hadda na islamiya inda yace idan makarantun Islamiya na kulle ta yaya yara zasu koyi Qur'ani?
Ƴansanda sun kama wani matashi kan zargin kashe mahaifiyarsa a Bauchi

Ƴansanda sun kama wani matashi kan zargin kashe mahaifiyarsa a Bauchi

Duk Labarai
Rundunar ƴansanda a jihar Bauchi ta ce ta kama wani matashi kan zargin kashe mahaifiyarsa. Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴansandan jihar, CSP Ahmed Wakili ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne ranar 24 ga watan Fabrairu a wata unguwa mai suna Abujan Kwata. Ya ce ana zargin matashin mai suna Safiyanu Dalhatu ɗan shekara 20, da amfani da taɓarya wajen lakaɗawa mahaifiyarsa duka har ta kai ga mutuwarta. "Matashin ya yi wa mahaifiyar tasa mai suna Salama Abdullahi mai shekara 40 munanan raunuka a hannu kuma ya yi mata jina-jina abin da ya kai ga mutuwarta," in ji sanarwar ƴansandan. CSP Wakili ya ce bayan samun rahoton abin da faru ne suka aika tawagar jami'ansu zuwa anguwar, inda suka ɗauki mahaifiyar matashin zuwa asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa - inda wani likita y...
Wannan abin kunya da yawa yake, A samu wasu su sasanta Sanata Natasha da Akpabio>>Inji Kungiyar Kiristoci ta CAN

Wannan abin kunya da yawa yake, A samu wasu su sasanta Sanata Natasha da Akpabio>>Inji Kungiyar Kiristoci ta CAN

Duk Labarai
Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN ta nemi a samu wasu su shiga tsakani kan rikicin dake faruwa tsakanin Sanata Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti. Shugaban kungiyar reshen Arewa da Abuja, Rev. John Joseph Hayab ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai,. Yace 'yan Najeriya na kallon 'yan majalisar da mutunci kada su bari lamarin ya canja. Yace kamata yayi a yi kokarin kare mutuncin 'yan majalisar dama 'yan Najeriya baki daya.
Kotu a Kano ta ɗaure ƴan TikTok biyu kan wallafa bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa

Kotu a Kano ta ɗaure ƴan TikTok biyu kan wallafa bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa

Duk Labarai
Wata kotun majistre da ke zama a anguwar Norman's land a karamar hukumar Fagge a jihar Kano, ta ɗaure wasu ƴan TikTok biyu a gidan yari, bayan samunsu da laifin amfani da bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa. Hukumar tace fina-finai ta jihar ta kama mutanen ne Ahmad Isa da Maryam Musa mazauna anguwar Ladanai da ke Hotoro Quarters, inda daga bisani ta miƙa su ga kotun, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito. Lauyan gwamnatin jihar ta Kano, Barrister Garzali Maigari Bichi, ya same su da aikata laifi da ya kunshi haɗa baki don aikata laifi da kuma wallafa hotunan bidiyo masu ɗauke da kalaman batsa a shafukan sada zumunta. Kotun ta ce bidiyon na rashin ɗa'a ya ci karo da addini da kuma tarbiyya a jihar ta Kano. Mutanen biyu sun amsa aikata laifin. Alkaliyar kotun, mai shar...

SAUKIN RAYUWA: Farashin Man Fetur Ya Ƙara Zaftarowa Kasa A Nijeriya

Duk Labarai
A wani yanayi na ƙara raguwar farashin kayan masarufi da abeben more rayuwa a Najeriya,Kamfanin Man Fetur na NNPCL, ya sanar da rage farashin man fetur daga Naira 920 zuwa Naira 860 kan ko wace lita. Wannan raguwar farashin ya biyo bayan rige-rigen sauke farashin kayayyaki dake gudana tsakanin yan kasuwanni wanda bai bar har dilolin man fetur ba, sakamakon tashin darajar Naira da ta fetur a kasuwannin duniya Sabon farashin kamfanin na NNPC, zai fara aiki a ranar Litinin mai zuwa. A makon da ya gabata ma, matatar mai ta Dangote ta rage farashin man fetur daga naira 890 a kowace lita zuwa naira 825, wanda hakan ya zamo karo na biyu da take rage farashin a wata ďaya kacal. A cikin sanarwar rage farashin da Kamfanin da na NNPCL ya fitar, ya sanar da wasu abokan huldarsa guda uku da...