Thursday, February 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Hotuna: Kwamandan Sojojin Najariya da aka kkashe tare da Wasu sojoji sama da 20 a jihar Borno

Kalli Hotuna: Kwamandan Sojojin Najariya da aka kkashe tare da Wasu sojoji sama da 20 a jihar Borno

Duk Labarai
Kwamandan sojojin Najariya na runduna na 149 dake Malam Fatori jihar Borno Lt. Col. TE Alari da aka kashe kenan a ranar 24 ga watan Janairu a wani mummunan hari da ya faru. An kashe shine tare da wasu manyan sojoji 2 da kuma sauran kananan sojoji 17. Ana zargin kungiyar B0k0 Hàràm da ISWAP ne suka kai harin. Saidai rahotanni sun banbanta kan yanda aka kai harin. Inda kafafen yada labarai da yawa sukace an kai harinne kan sansanin sojojin dake garin Malam Fatori dake iyakar Najeriya da Nijar, a bangare guda kuma, shahararren me watsa labarai na tsaro, Zagazola Makama ya ruwaito cewa harin kunar bakin wakene aka kai kan tawagar kwamandan. Saidai abu daya daya tabbata shine an kai harin kuma an kashe sojojin.
Gyaran Najeriya sai Allah>>Inji Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari

Gyaran Najeriya sai Allah>>Inji Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari

Duk Labarai
Tsohon Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, Allah ne kadai da ya halicci Najeriya zai iya gyarata. Ya bayyana hakane a wajan wani taron Jam'iyyar APC da ya gudana a jihar Katsina ranar Asabar data gabata inda masoyansa da yawa suka taru. Wannan kalamai nasa sun jawo suka da Allah wadai musamman daga 'yan jam'iyyun adawa da kungiyoyin fafutuka. Misali kakakin Jam'iyyar NNPP, Ladipo Johnson ya bayyana cewa, Jam'iyyar APC yaudarar 'yan Najeriya ta yi duk da cewa ta san bata san hanyar da zata warware matsalolin Najeriya ba amma ta karbi ragamar aikin. Ya kara da cewa, wannan magana da tsohon shugaban kasar yayi alamace ta cewa APC ta gaza kuma ba zasu iya magance matsalar Najeriya ba inda suka jawowa kasar koma bayan tattalin arziki, ya kuma ce hakan na nuni da cewa ko...
‘Yan kasuwar man fetur zasu daina sayen man fetur din daga matatar man Dangote inda zasu koma shigo dashi daga kasar waje saboda yafi Arha

‘Yan kasuwar man fetur zasu daina sayen man fetur din daga matatar man Dangote inda zasu koma shigo dashi daga kasar waje saboda yafi Arha

Duk Labarai
' Yan kasuwar man fetur zasu daina sayen man fetur daga matatar man fetur ta Dangote inda zasu rika shigo dashi daga kasashen waje saboda na kasar wajen ya fi arha. Rahotanni sun bayyana cewa idan 'yan kasuwar suka shigo da man fetur din daga kasar waje har ya zo Najeriya zai zo musu ne akan farashin Naira N922.65 akan kowace lita, wannan farashin ya hada da duka farashin jirgin ruwa da ya dakko man fetur din da canjin dala da aka yi da kudin haraji da komai da komai. Saidai idan kuma zasu sayi man a hannun matatar man Dangote zasu sayeshi ne akan farashin Naira N955 akan kowace lita. Hakan yana nufin sun samu saukin Naira N32.35 idan suka sayi man fetur din daga kasashen waje maimakon matatar man fetur ta Dangote. Daya daga cikin 'yan kasuwar da bai so a bayyana sunan...
Umma Shehu Ta Sake Sawa An Kama Wani Mai Suna Aminu BBC Wanda Ya Jadadda Maganganun Da Shehun Tikțok Ya Yi Akanta

Umma Shehu Ta Sake Sawa An Kama Wani Mai Suna Aminu BBC Wanda Ya Jadadda Maganganun Da Shehun Tikțok Ya Yi Akanta

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Umma Shehu Ta Sake Sawa An Kama Wani Mai Suna Aminu BBC Wanda Ya Jadadda Maganganun Da Shehun Tikțok Ya Yi Akanta. https://www.tiktok.com/@aminu_b.b.c/video/7462133354872327429?_t=ZM-8tPNqGEDybd&_r=1 https://www.tiktok.com/@aminu_b.b.c/video/7462244036234054917?_t=ZM-8tPO1KqBH0Q&_r=1 Ga bidiyoyin da suka jawowa Aminu BBC da Umma Shehu rashin fahimtar juna.
Hotuna: Me wasan barkwanci na Najeriya, Zicsaloma ya je kasar Turkiyya inda likitoci suka mikar masa da hancinsa

Hotuna: Me wasan barkwanci na Najeriya, Zicsaloma ya je kasar Turkiyya inda likitoci suka mikar masa da hancinsa

Duk Labarai
Me wasan Barkwanci a Najeriya, Zicsaloma ya je kasar Turkiyya inda likitoci suka mikar masa da hancinsa. Zicsaloma ya hau shafinsa na sada zumuntar Instagram inda ya bayyana hakan. Kuma ya bayyana cewa,mikar da hancinsa abune da ya dade yana ta kokarin yi. Ya bayyana cewa, likitocin sun gaya masa sai an tada wasu komada a fuskarsa kamin a samu damar yi masa gyaran fuskar kuma tuni ya amince da hakan.
An kama me gàrkùwà da mutane bayan da ya kai ziyarar jaje ga wanda ya sace har gida

An kama me gàrkùwà da mutane bayan da ya kai ziyarar jaje ga wanda ya sace har gida

Duk Labarai
Mahukunta a garin Kwantagora dake jihar Naija sun kama wani me garkuwa da mutane. Kakakin 'yansandan jihar, SP Wasiu Abiodun ya tabbatar da kamen a karshen makon da ya gabata, yace wanda ake zargin, Nasiru Isyaka na tare da wasu gungun masu garkuwa da mutanene da suka kai hari kauyen Sabon-Gari Mangu Matachibu inda suka kashe mutum daya da yin garkuwa da wasu biyu. Nasiru Isyaka dai shima dan garin Sabon-Gari Mangu Matachibu kuma bayan da aka kubutar da wadanda suka yi garkuwa dasu, ya je yi masa jaje inda a nan ne ya ganeshi. Ya kara da cewa an kwace bindiga hadin gida guda daya daga hannunsa sannan kuma ya amsa laifin da ake zarginsa dashi.
Wani gurin Ibada ya bayyana a Legas inda musulmai da kirista ke zuwa suna ibada tare

Wani gurin Ibada ya bayyana a Legas inda musulmai da kirista ke zuwa suna ibada tare

Duk Labarai
Wani guri da ake kira da Jehova Allah a Legas ya bayyana inda musulmai da Kiristoci ke haduwa su yi Ibada. Gurin ana karatun Qur'ani a cikin sa sannan ana wakewake da addu'a irin ta Kiristanci. Lamarin ya baiwa mutane mamaki sosai musamman ganin yanda ba kasafai aka cika samun irin wannan hadaka ba a kasarnan. Rahoton jaridar Punchng yace an gina wajan ne shekaru 12 da suka gabata dan samar da hadin kai tsakanin musulmai da kirista.
Mun daina fargabar da muke yi akan Muslim-Muslim saboda Gwamnatin Tinubu ta mana Adalci>>Inji Kungiyar Kiristanci ta CAN

Mun daina fargabar da muke yi akan Muslim-Muslim saboda Gwamnatin Tinubu ta mana Adalci>>Inji Kungiyar Kiristanci ta CAN

Duk Labarai
Kungiyar kiristoci ta CAN ta bayyana cewa, sun daina bargabar da suke akan mulkin Muslim-Muslim. Kungiyar reshen Arewa ce ta bayyana hakan ta bakin shugabanta, Reverend Yakubu Pam. Ya bayyana cewa a yanzu sun daina Adawa da Gwamnatin ta Tinubu saboda yanda ta kewa kowane addini Adalci. Yace amma har yanzu suna kira ga Gwamnatin data baiwa kirista babban mukami dan ya wakilci bangaren kiristocin kasarnan.