Monday, February 16
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima sun kashe Naira Biliyan 8.64 wajan tafiye-tafiye kadai a cikin watanni 3 da suka gabata

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima sun kashe Naira Biliyan 8.64 wajan tafiye-tafiye kadai a cikin watanni 3 da suka gabata

Siyasa
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima sun kashe Naira Biliyan 8.64 wajan tafiye-tafiye a cikin watanni 3 kacal da suka gabata. An gano hakanne ta hanyar Amfani da wata manhaja me suna Govspend da ake amfani da ita wajan bibiyar kudaden da gwamnati ke kashewa. Hakanan an gano cewa an kashe Naira Biliyan 12.59 wajan kula da jiragen da suka yi amfani dasu wajan yin wadannan tafiye-tafiye.
Kalli Hotuna da Bidiyo: Ali Jita ya je filin wasan Wembley dake Landan kasar Ingila kallon wasan karshe na Champions League tsakanin Real Madrid da Borussia Dortmund

Kalli Hotuna da Bidiyo: Ali Jita ya je filin wasan Wembley dake Landan kasar Ingila kallon wasan karshe na Champions League tsakanin Real Madrid da Borussia Dortmund

Ali Jita, Kannywood
Tauraron mawakin Hausa, Ali Jita ya halarci Filin Wembley dake birnin Landan kasar Ingila da yammacin jiya inda aka buga wasan karshe na gasar Champions League tsakanin Real Madrid da Borussia Dortmund. Jiya ya wallafa bidiyo da hotunansa a cikin filin wasan a shafukansa na sada zumunta: https://twitter.com/alijitaa/status/1796981621461025021?t=OU25PygGuJxpRFuRPbBLGw&s=19
Mutane na cikin wahala da Yunwa a Najeriya>>Obasanjo

Mutane na cikin wahala da Yunwa a Najeriya>>Obasanjo

Siyasa
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa, mutane na cikin wahala da yunwa a Najeriya. Ya bayyana hakane a legas wajan wani taro da aka gayyaceshi. Obasanjo yace matsalar tsaro ce ta daidaita kasarnan sannan ya koka da matsalar rashin shugabanci na gari. Yayi kira ga shuwagabannin kasar da su tashi tsaye wajan inganta rayuwar mutane. Yace akwai bukatar canja Shuwagabanni wanda zasu kawo ci gaba irin wanda ake bukata.

Yadda ake fara soyayya

Duk Labarai
A addinance, idan ka ga yarinya, Budurwa kana so, zaka fara zuwa wajan mahaifinta ne ka nemi izini. Idan kuma ba zaka iya zuwa ba kai tsaye, zaka iya aika magabatanka a nemar maka izini idan ba'a bayar da ita ba. Idan ka samu aka maka iso to aiki ya ganka. Anan ne kai kuma aiki ya rage gareka ka samu hanyar da zaka yi nasara soyayyarka ta shiga zuciyarta. Abubuwan da zaka rika yi dan jan hankalinta: Ka rika yin kwalliya sosai idan zaka je wajenta. Ka rika saka turare. Ka wanke baki. Ka rika bata labarin abinda bata sani ba. Ka rika mata kyauta. Ka rika kokarin sata dariya. Ka mayar da ita abokiyarka, ka rika neman shawarar ta. Wannan zai sa ka shiga zuciyarta sosai kuma itama ta ji tana sonka.
MASANA’ANTAR KANNYWOOD WAJE NE NA GYARA TARBIYYA BA GURƁATA WA BA, CEWAR MARYAM SANI

MASANA’ANTAR KANNYWOOD WAJE NE NA GYARA TARBIYYA BA GURƁATA WA BA, CEWAR MARYAM SANI

MARYAM SANI
Wata sabuwar Jaruma a masana'antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Maryam Muhammad Sani ta bayyana Kannywood ɗin a matsayin wata masana'anta wacce ake faɗakarwa da gyaran tarbiyyar al'umma ba wai ɓata tarbiyya ba. Maryam ta bayyana haka ne ta cikin wata tattaunawarta da Jaridar Dokin Ƙarfe TV inda ta ƙara da cewa "Na shigo masana'antar Kannywood ne domin ina da gudunmawar da zan bayar game da gyaran tarbiyyar al'ummar nan tamu". In jita. Maryam ta kuma ƙara da cewa "Bai kamata mutane suna ƙyamatar ƴan fim ba. Domin fim harka ce ta kawo cigaba da magance matsalar tsaro da raya al'adun Hausa Fulani". A cewar ta. Daga ƙarshe Malama Maryam ta kuma ƙara da cewa tarbiyya tana farawa ne tun daga gida, dan haka masana'antar Kannywood waje ne na koya tarbiyya ba ɓatawa ba". In ji ta....
Kalli Kuga: Kungiyar Hezbollah ta sanar da lalata babban makamin kasar Israela me suna Iron Dome da take amfani dashi wajan tare makaman da ake harba mata

Kalli Kuga: Kungiyar Hezbollah ta sanar da lalata babban makamin kasar Israela me suna Iron Dome da take amfani dashi wajan tare makaman da ake harba mata

Labaran Falasdinawa, Labarin Yakin Gaza, Yakin gaza da isra'ila
Kungiyar Hezbollah ta kasar Lebanon ta sanar da kaiwa babban makamin da kasar Israela take ji dashi wajan tare makaman da ake aika mata me suna Iron Dome. Hezbollah tace ta aikawa Iron Dome bamabamai ne wanda ya lalatashi da kuma kashe ko kuma raunata sojojin dake kula dashi.
Kalli Hoto: Tsohuwar ‘yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Kalli Hoto: Tsohuwar ‘yar kwallon Najeriya da Tsohon Gwamnan Kaduna Malam Nasiru Ahmad ya dauki nauyinta zuwa kasar Amurka aka mata aiki ta koma Namiji na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan a mata karin aikin da zata rika haihuwa

Duk Labarai
Tsohuwar 'yar kwallon Najeriya, Iyabo Abade wadda yanzu Namiji ce da sunan James Johnson na neman taimakon Naira Miliyan 69.7 dan ta samu ta rika haihuwa. Iyabo ta bugawa Najeriya was a tsakanin 1997 da 2000. Kuma a shekarar 2004 ne aka canja mata halitta a kasar Amurka ta koma Namiji. Tsohon ministan babban birnin tarayya a wancan lokacin, Malam Nasiru El-Rufai ne ya dauki nauyin aikin da aka mata. Saidai kamin kace wani abu, Ita dai Iyabo an haifeta ne a matsayin mata maza, watau tana da azzakari da farji irin na mata. Dan hakane ta zabi daya ko kuma aka duba wanda yafi karkata aka gano Namiji ne kuma aka mata aiki ta koma cikakken Namiji. Saidai tana bukatar a kara mata aiki dan ta samu ta rika haihuwa.