Friday, December 5
Shadow

Ba gaskiya bane, Ban ce zan janye wa kowa daga takarar shugaban kasa ba>>Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya musanta rahotanni dake yawo cewa wai yace zai janye wa matashi yayi takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC.

Atiku ta bakin me magana da yawunsa, Paul Ibe yace wannan magana ba gaskiya bace.

Yace a hirar da yayi da BBC babu inda yace zai janyewa wani dan takara, yace abinda ya fada shine idan aka yi zaben fidda gwani kuma matashi yayi nasara a zaben zai goya masa baya.

Atiku yayi kira ga ‘yan Jarida su daina fassara labari ba yanda ya kamata ba.

Karanta Wannan  Tabbas Goodluck Jonathan zai tsaya takarar shugaban kasa a 2027 a jam'iyyar PDP>>Farfesa Jerry Ghana

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *