Wednesday, April 29
Shadow

Ba gaskiya bane, Ban ce zan janye wa kowa daga takarar shugaban kasa ba>>Atiku Abubakar

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya musanta rahotanni dake yawo cewa wai yace zai janye wa matashi yayi takarar shugaban kasa a jam’iyyar ADC.

Atiku ta bakin me magana da yawunsa, Paul Ibe yace wannan magana ba gaskiya bace.

Yace a hirar da yayi da BBC babu inda yace zai janyewa wani dan takara, yace abinda ya fada shine idan aka yi zaben fidda gwani kuma matashi yayi nasara a zaben zai goya masa baya.

Atiku yayi kira ga ‘yan Jarida su daina fassara labari ba yanda ya kamata ba.

Karanta Wannan  Allah Sarki: Kalli Bidiyonsa inda ya fashe da kuka bayan da ya dauki kudin da ya dade yana tarawa ya buga càcà cewa Manchester City zata ci Manchester United

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *