Tuesday, April 7
Shadow

Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa da ake shirin yi.

Shugaban hukumar NCC, Aminu Maida ne ya bayyana hakan a yayin zantawa da manema labarai.

Yace karin harajin kaso 5 akan kamfanonin sadarwar yana kunshene a cikin sabon kudirin dokar da majalisa ta amince dashi.

Yace yana wajan aka kawowa shugaba Tinubu maganar karin amma yace ba zai kara saka ‘yan Najeriya a cikin matsala ba.

Yace a baya an dakatar da karinne amma yanzu an cireshi gaba daya.

Karanta Wannan  Ban taba ganin Mutum Irin Shehu ba, Gaba daya gidajensa baya sa Haya, Kyauta yake ba mutane su zauna>>Inji Matar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *