Saturday, January 3
Shadow

Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa da ake shirin yi.

Shugaban hukumar NCC, Aminu Maida ne ya bayyana hakan a yayin zantawa da manema labarai.

Yace karin harajin kaso 5 akan kamfanonin sadarwar yana kunshene a cikin sabon kudirin dokar da majalisa ta amince dashi.

Yace yana wajan aka kawowa shugaba Tinubu maganar karin amma yace ba zai kara saka ‘yan Najeriya a cikin matsala ba.

Yace a baya an dakatar da karinne amma yanzu an cireshi gaba daya.

Karanta Wannan  Ya Kamata Yayana Dauda Kahutu Rarara Shugaban Kasar Mawakan Nijeriya, Ya Yi Min Kara Ya Wake Ni Saboda Irin Kaunar Da Nake Yi Wa Shugaban Kasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Cewar Khamis Musa Darazo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *