Saturday, December 13
Shadow

Babu Alamar Abubuwa zasu yi sauki a gwamnatin Tinubu>>Inji Archbishop Nwaobia

Wani babban malamin Kiristanci Archbishop Nwaobia ya bayyana cewa babu alamar lamura zasu gyaru a gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.

A hirar da wakilin jaridar sunnewsonline suka yi dashi, ya bayyana cewa faduwar darajar Naira akan Dalar Amurka matsala ce babba wadda ta jefa ‘yan Najeriya da yawa cikin halin wahala.

Yace kuma gwamnatin Tinubu ta kasa samo hanyar warware wannan matsala.

Ya kara da cewa, Sam Gwamnatin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu bata da alkibla dan ta kasa dasa tushen ci gaban Najeriya.

Karanta Wannan  Tsadar rayuwa: Tsohon Gwamnan jihar Sokoto Alhaji Aminu Waziri Tambuwal ya ce sai da suka yi wa 'yan Nijeriya gargadi kar su sake yin kuskuren zaben jam'iyyar APC a zaben 2023

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *