Saturday, December 13
Shadow

Babu wata data fita daga Musulunci zuwa Kirista>>Gwamnatin Jihar Zamfara

Gwamnatin Zamfara ta karyata labarin dake cewa wata me suna Zainab ta fita daga Musulunci zuwa Kirista a jihar.

Me magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Yace sun yi bincike ta hanyar kiran Alkalin Alkalai na jihar da kiran dukkan masu ruwa da tsaki na jihar kan bangaren shari’a duk sun tabbatar musu babu wata me suna Zainab data canja addini.

Dan haka ya bayyana cewa labarin karyane wadda wata kafar yada labarai ta yanar gizo ta wallafa dan neman mabiya.

Karanta Wannan  Abin a Yaba: Ya tsinki Dala $10,000 kwatankwacin Naira Miliyan 15 a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano ya mayarwa mesu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *