Wednesday, April 29
Shadow

Babu yarjejeniyar yin karɓa-karɓa tsakanina da Atiku – Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya musanta raɗe-raɗin da ke cewa an cimma yarjejeniya tsakaninsa da tsofaffin ƴan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyun hamayyar ƙasar – Atiku Abubakar na PDP da Peter Obi na LP – kan cewa kowannensu zai yi mulki na wani wa’adi.

A hirarsa da BBC, Kwankwaso ya ce bai san da maganar ba, amma ya samu labarin cewa ɓangaren Atikun na ta “yin taruka da shugabannin yankin ciki har da malamai, suna faɗa masu wannan magana”.

Karanta Wannan  Da na so zama shugaban kasa a karo na 3, nasan yanda zan yi in samu, babu wanda ya isa ya hanani>>Inji Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *