
A jiyane dai Limaman Darika suka kaiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ziyara a fadarsa dake Abuja.
A cikin tawagar akwai manyan malaman Darika daga kasashen Algeria, Senegal da Najeriya.
A Bidiyon da ya bayyana na bayan Taro, An ga yanda suka gayawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa, yana kokari a bangaren tsaro amma suna kira a gareshi da ya kara kaimi.