Sunday, May 25
Shadow

Duk Labarai

WATA SABUWA: Laifi Mijin Hussaina Yayi, Afuwa Ya Kamata A Nema Masa, Cewar Jamila Ibrahim

WATA SABUWA: Laifi Mijin Hussaina Yayi, Afuwa Ya Kamata A Nema Masa, Cewar Jamila Ibrahim

Duk Labarai
Jamila Ibrahim ta ce; "Wani babban soja ya kirani munyi magana fiye da minti 30 akan maganar Seaman Abbas, jikina yayi sanyi sosai wlh… "Magana ta Allah kar ayi using ƙarfi da viol*ence inba hakan ba za'a ƙara implicating ɗinsa ne, a nemi afuwa kawai a sassauta masa. "A doka abinda yayi zai iya daɗewa sosai a garƙame ba'aji ɗuriyarsa ba… "Da farko cikin laifinsa da aka bayyana min ba masallaci yaje ba, Brigade MS zaiyi addressing ɗinsu da safe misalin ƙarfe 10 na safe baizo da wuri ba sai Abbas da abokinsa suka fita basu dawo ba sai da aka gama addressing sauran mutanen… "Da aka hango shi yana zuwa ogansa yace daga ina yake bai amsa ba, akace masa you're stup!d yace he's not stup!d dey should address him by his name and rank, nan ne ran ogansa ya ɓaci yace ayi disarming ...
ALLAHU AKBAR: An Yi Jana’izar Mutane 41 Da Sùķa Ŕaśù Sakamakon Hàďaŕìn Moțà A Hanyar Su Ta Zuwa Wajen Zagayen Mauĺùďì Daga Garin Kwandari Zuwa Samunaka

ALLAHU AKBAR: An Yi Jana’izar Mutane 41 Da Sùķa Ŕaśù Sakamakon Hàďaŕìn Moțà A Hanyar Su Ta Zuwa Wajen Zagayen Mauĺùďì Daga Garin Kwandari Zuwa Samunaka

Duk Labarai
An Yi Jana'izar Mutane 41 Da Sùķa Ŕaśù Sakamakon Hàďaŕìn Moțà A Hanyar Su Ta Zuwa Wajen Zagayen Mauĺùďì Daga Garin Kwandari Zuwa Samunaka Mahalarta mauludin sun yi gamu da ajalin na su ne a jiya Lahadi, a loķacin da motar su ta yi arañģàmà da tireĺa a daidai garin Lere, inda kimanin mutane talatìn sùka mùțù nañ take, yayin da kaŕin mutane sha daya suka ŕaśu bayan an kai su asibiti domin jinyar su sakamakon raunin da suka samu. Allah Ya gafarta musu. Daga Umar Isa Ramin Kura
Kwamitin kula da sha’anin sojojin ruwa (Navy) na majalisar dokoki ta tarayya sun gana da hukumar Sojin ruwa domin binciko zargin yadda aka ci zarafin Seaman Abbas Haruna

Kwamitin kula da sha’anin sojojin ruwa (Navy) na majalisar dokoki ta tarayya sun gana da hukumar Sojin ruwa domin binciko zargin yadda aka ci zarafin Seaman Abbas Haruna

Duk Labarai
Kwamitin kula da sha'anin sojojin ruwa (Navy) na majalisar dokoki ta tarayya sun gana da hukumar Sojin ruwa domin binciko zargin yadda aka ci zarafin Seaman Abbas Haruna tsawon shekara 6 bisa umurnin wani babban jami’in Jeneral MS Adamu. Majalisar ta lashi takobin yin binciken ƙwakwaf akai domin hukunta duk wanda aka samu da laifi a lamarin Wane fata zaku yi musu ?
‘Muna fargabar barkewar cutuka masu muni a Maiduguri’

‘Muna fargabar barkewar cutuka masu muni a Maiduguri’

Duk Labarai
Masana harkokin lafiya a Najeriya sun yi kira ga gwamnatin kasar da ta aike da tawagar likitoci na musmaman da suka kware kan cututuka masu yaɗuwa zuwa Borno saboda fargabar barkewar cututuka sakamakon ambaliyar ruwan da aka fuskanta a jihar. Masanan sun ce, suna fargabar barkewar cututuka irinsu zazzabin cizon sauro, da Zika, da zazzabin typoid, da na dange, da kuma uwa uba amai da gudawa, sakamakon irin dattin da ambaliyar ruwa ta kwaso da gawarwakin makabartu da ruwan ya dauko. Dr Nasiru Sani Gwarzo, babban sakataren ma'aikatar Ilimi a Najeriya, kuma masani kan harkokin kiwon lafiya ya shaida wa BBC cewa, dole ne hukumomi su gaggauta shawo kan ruwan da ya malale asibitin koyarwa na Maiduguri saboda wasu daga cikin na'urorin asibitin akwai wadan ke da sinadarin nukiliya a ciki da k...
Dangote ya karyata maganar NNPCL cewa a farashin Naira 898 ya sayar musu da man fetur

Dangote ya karyata maganar NNPCL cewa a farashin Naira 898 ya sayar musu da man fetur

Duk Labarai
Matatar man fetur ta Dangote ta musanta ikirarin kamfanin mai na kasa,NNPCL da yace ya sayo mai na farko daga Dangote akan farashin Naira 898 akan kowace lita. Me magana da yawun kamfanin,Mr Olufemi Soneye ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Yace da dala aka sayar musu da danyen man fetur dun da suka saya dan haka suma da dala suka sayarwa da kamfanin na NNPCL da tataccen man fetur din. Ya bayyana cewa kuma mansu zai isa kowane sako da lungu na kasarnan. Yace a saurari kwamitin da shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya kafa kan lamarin shine zai bayyana farashin man nasu.