Thursday, March 26
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Gwamnatin Jihar Kano ta dauki mataki akan Malam Lawal Triumph, saidai bai yiwa dalibansa dadi ba

Da Duminsa: Gwamnatin Jihar Kano ta dauki mataki akan Malam Lawal Triumph, saidai bai yiwa dalibansa dadi ba

Duk Labarai
DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnatin Kano ta dakatar da Malam Lawan Triumph daga yon wa'azi Majalisar Shura da gwamnatin Kano ta kafa ta sanar da dakatar da Malam Lawan Shuaibu Triumph daga yin wa'azi. A wani taron manema labarai da Sakataren majalisar, Alhaji Shehu Wada Sagagi ya yi a yau Laraba, ya ce an dakatar da Malam Lawan ne domin bashi damar ya zo gaban majalisar ya kare kan sa daga zarge-zargen da ake yi masa na yin kalaman ɓatanci ga Ma'aiki. A cewar Sagagi, an dakatar da Malam Lawan har sai an kammala bincike da jin ta bakin sa a matakin Majalisar ta shura. Ya kuma yi kira ga ƴan siyasa da su guji tsoma baki a batun, inda ya bukaci da a kyale kwamitin ya kammala aikin sa. Sagagi ya tabbatar da cewa Majalisar za ta yi aiki tsakani da Allah ba tare da son rai ko rashin adalci ba...
Kalli Bidiyo:Jama’ar Katsina ku yi Hakuri, kamin in hau mulki na yi Alkawarin duk wata zan rika bada bayanin yawan kudaden da muka samu da yawan wanda muka kashe, amma yanzu da na zama Gwamnan naga abin ba zai yiyu ba>>Inji Gwamnan Jihar Katsina Dikko Radda

Kalli Bidiyo:Jama’ar Katsina ku yi Hakuri, kamin in hau mulki na yi Alkawarin duk wata zan rika bada bayanin yawan kudaden da muka samu da yawan wanda muka kashe, amma yanzu da na zama Gwamnan naga abin ba zai yiyu ba>>Inji Gwamnan Jihar Katsina Dikko Radda

Duk Labarai
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Radda ya baiwa al'ummar Jihar Hakuri inda yace kamin ya hau mulki yayi Alkawarin rika bayar da ba'asi kan yawan kudaden da aka samu da wanda aka kashe. Yace amma bayan da ya hau yaga abin ba mai yiyuwa bane. Gwamnan yace dalili kuwa shine Wasu kudaden idan aka karbosu kudin aikin gwamnatin data wucene za'a biya, hakanan wasu kudaden kuma aikin da aka yi shekarar data wucene za'a biya dasu. A karshe dai yace shima dan Adam ne dan haka yana neman Afuwa. Kalli Bidiyon jawabinsa a kasa; https://www.tiktok.com/@mps_mediang/video/7553746884012035346?_t=ZS-90BqPMn9FZ3&_r=1
Mun samar da tsaro sosai a Yankin Arewa, yanzu mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu, sun koma garuruwansu>>Inji Shugaba Tinubu

Mun samar da tsaro sosai a Yankin Arewa, yanzu mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu, sun koma garuruwansu>>Inji Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, jami'an tsaro sun samar da tsaro sosai a yankin Arewa maso gabas da Arewa maso yamma. Yace Mutanen da a baya suka tsere daga gidajensu saboda matsalolin tsaro a yanzu sun koma gidajen nasu. Shugaban yace an samu nasarori sosai a yaki da masu dauke da makamai a sassa daban-daban na kasarnan. Shugaban ya bayyana hakane yayin da yake jawabin ranar cikar Najeriya shekaru 65 da samun 'yanci. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1973276459851718762?t=kes68RdXaxTNIpxXB9Z7OQ&s=19
Kalli Bidiyo: Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce Kwamishinan ‘yansandan Kanon ya basu kunya kuma suna Allah wadai da abinda yayi na kin Halartar Bikin ‘yancin Najeriya

Kalli Bidiyo: Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce Kwamishinan ‘yansandan Kanon ya basu kunya kuma suna Allah wadai da abinda yayi na kin Halartar Bikin ‘yancin Najeriya

Duk Labarai
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya yi Allah wadai da kwamishinan 'yansandan jihar, Inda yace ya basu kunya saboda kin halartar bikin ranar 'yancin Najeriya. Gwamna Abba yace Kwamishinan ya dauki matakai da suka nuna cewa yana goyon bayan wata jam'iyya. Gwamnan yace shine Gwamna sannan shugaban tsaro na jihar Kano kuma Allah ne ya bashi, dan haka babu wanda ya isa ya kwace mai. Gwamnan yayi kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya cire Kwamishinan 'yansandan daga jihar Kano na kawo musu wani. Kalli Jawabin Gwamnan a kasa: https://www.tiktok.com/@sardauna_shoot.ng/video/7556210141406711048?_t=ZS-90BmkqFaY76&_r=1
Daga yau, 1 ga watan Oktoba, hukumar shige da fici ta Najeriya zata fara kama ‘yan kasar waje dake zaune a Najeriya ba bisa ka’ida ba, ko wadanda suka shigo Najeriya ba tare da takardu ba

Daga yau, 1 ga watan Oktoba, hukumar shige da fici ta Najeriya zata fara kama ‘yan kasar waje dake zaune a Najeriya ba bisa ka’ida ba, ko wadanda suka shigo Najeriya ba tare da takardu ba

Duk Labarai
Rahotanni sun ce daga yau, 1 ga watan Oktoba, Hukumar kula da shige da fici ta Najeriya zasu fara kame da hukunta wadanda suka shigo Najeriya bizarsu ta kare basu fita ba da wadanda kuma suna shigo ba tare da takardu ba. Wadanda aka kama da laifi, zasu iya fuskantar hukuncin mayar dasu kasashensu ko kuma cinsu tara. Wanda aka kama ya dade a Najeriya tsawon watanni 3 bayan shigowa kuma takardunsa sun kare, zai biya tarar Dala $15 kullun. Ko kuma a bashi zabin hanashi shigowa Najeriya na tsawon shekaru 2. Sai kuma wadanda suka tsaya a Najeriya na tsawon watanni 3 zuwa shekara 1, su kuma za'a musu hukuncin biyan tarar dala $15 kullun ko kuma hanasu shigowa Najeriya na tsawon shekaru 5.
Kalli Bidiyo: Ta je Saudiyya tana rokon Allah ya hana Salisu Umar Salinga Kwanciyar Hankali har sai ya biya mahaifiyarta kudadenta

Kalli Bidiyo: Ta je Saudiyya tana rokon Allah ya hana Salisu Umar Salinga Kwanciyar Hankali har sai ya biya mahaifiyarta kudadenta

Duk Labarai
Wannan matashiyar ta je Saudiyya a dakin Ka'aba tana rokon Allah ya hana Salisu Umar Salinga Kwanciyar Hankali. Tace Allah ya hanashi abinda yake so har sai ya biya mahaifiyarta kudin ta dake hannunsa. Saidai da yawa sun bayyana cewa irin wannan addu'a da ta yi bata dace ba. https://www.tiktok.com/@realgudgirl0/video/7554450456676764936?_t=ZS-90BWkcIbgqO&_r=1
Karanta Jadawali: An fitar da bayanin Jihohin da dalibai suka fi karbar bashin karatu na NELFUND na Gwamnatin Tarayya

Karanta Jadawali: An fitar da bayanin Jihohin da dalibai suka fi karbar bashin karatu na NELFUND na Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, an fitar da bayanin jihohin da dalibai suka fi karbar Bashin Karatu na Gwamnatin Tarayya da ake kira da NELFUND. Jihohin sune kamar haka: 1. Borno: 61,3842. Kano: 57,9833. Kaduna: 45,0024. Katsina: 43,6025. Oyo: 33,2236. Bauchi:33,0277. Kwara: 31,6408. Plateau: 31,3149. Gombe: 31,30810. Taraba: 26,505
PENGASSAN ta amince ta janye yajin aiki bayan Dangote ya amince ya mayar da ma’aikata 800 da ya kora bakin aiki

PENGASSAN ta amince ta janye yajin aiki bayan Dangote ya amince ya mayar da ma’aikata 800 da ya kora bakin aiki

Duk Labarai
Ƙungiyar manyan ma'aikatan man fetur da iskar gas ta Najeriya, PENGASSAN ta amince da jingine yajin aikin da shiga bayan samun saɓani da matatar mai ta Dangote Yajin aikin na zuwa ne bayan PENGASSAN ta zargi mattaar da korar fiye da ma'aikata 800 saboda sun nuna sha'awar shiga ƙungiyar. Gwamnatin Najeriya ce ta shiga tsakani a sasancin ɓangarorin biyu da ake yi tun ranar Litinin, to amma sai a yau Laraba ne aka cimma matsaya. Cikin wata sanarwa da ma'aikatar kwadagon ƙasar ta fitar ta ce matatar ta amince da mayar da ma'aikatan da ta kora domin su ci gaba da aiki da ita. "Babu ma'aikacin da zai cutu sakamakon saɓanin matatar Dangote da PENGASSAN," a cewar sanarwar. A nata ɓangare, ƙungiyar ta PENGASSAN ta ''amince ta fara shirye-shiryen janye yajin aikin''. Tun bayan fara...
Kalli Bidiyo: Dan Allah duk wanda muka yi fada dashi, dan Darajar wannan dakin ya yafe min>>Inji Hassan Make-Up

Kalli Bidiyo: Dan Allah duk wanda muka yi fada dashi, dan Darajar wannan dakin ya yafe min>>Inji Hassan Make-Up

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Hassan Make-Up ya bayyana cewa, yana neman Afuwar duk wanda suka yi fada dashi ya yafe masa. Ya bayyana hakane yayin da yake kusa da ka'aba yake rokon dan darajar dakin Ka'aban duk wanda suka yi fada dashi ya yafe masa. A baya dai an ga Hassan Make-Up har kuka ya rika yi bayan da ya samu zuwa Aikin Umrah. https://www.tiktok.com/@officielhassanmakeup227/video/7555127311583038776?_t=ZS-90A3JHC3sYq&_r=1