Tuesday, December 16
Shadow

Duk Labarai

Gwamnatin tarayya zata gyarawa ma’aikata tsarin Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya zata gyarawa ma’aikata tsarin Kiwon Lafiya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta sanar da shirin gyarawa ma'aikatan ta tsarin kiwon lafiyarsu. Gwamnatin tace hakan ya zama dole musamman lura da hauhawar farashin magunguna. Gwamnatin ta bayyana hakane a yayin gwaji kyauta da kawa ma'aikatan a lokacin bikin satin ma'aikata a Abuja. Shugabar ma'aikatan gwamnatin tarayya, Mrs Didi Walson-Jack ce ta bayyana hakan a wajan inda tace kula da lafiyar ma'aikatan na da muhimmanci musamman lura da muhimmancin aikin da suke. Tace tsarin da ake kai a yanzu ya zama tsohon yayi yana da kyau a sake dubawa dan sabuntashi.
Wata Sabuwa: Ashe Ashe Daloline ake zargin Ganduje ya karba ya tafka magudin zabe shiyasa Tinubu ya tursasa masa sauka, ji cikakken labarin

Wata Sabuwa: Ashe Ashe Daloline ake zargin Ganduje ya karba ya tafka magudin zabe shiyasa Tinubu ya tursasa masa sauka, ji cikakken labarin

Duk Labarai
Bayan da shugaban jam'iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya ajiye mukaminsa da kuma bayyana cewa zai kula da lafiyarsa ne. Bayanai na ci gaba da fitowa kan ainahin dalilin da yasa ya sauka daga mukamin nasa. Rahoton majiyarmu yace Ganduje ya Zaben babban birnin tarayya, Abuja da aka yi, an zargi Ganduje da karbar kudi ya baiwa wanda yafi bayar da kudi takarar zabe. Rahoton yace bayan kammala zaben ne wasu suka shigar da korafi inda shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yasa a yi bincike. Bayan gabatarwa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sakamakon binciken ne sai ya kira taron kungiyar Gwamnonin APC inda ya shaida musu halin da ake ciki. Sannan aka nada wasu wakilai daga cikin gwamnonin ciki hadda Mai Mala Buni suka samu Ganduje suka gaya masa ya sauka girma da arziki ko a...
Ku Daina zabar shuwagabanni saboda addini ko kabilanci ku rika zabe saboda cancanta>>Tsohon Shugaban kasaz Jonathan ya baiwa matasa shawara

Ku Daina zabar shuwagabanni saboda addini ko kabilanci ku rika zabe saboda cancanta>>Tsohon Shugaban kasaz Jonathan ya baiwa matasa shawara

Duk Labarai
Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya baiwa matasan Najeriya shawarar su daina zaben shugaban kasa bisa banbancin Addini ko Kanilanci. Yace su rika zabe saboda cancanta. Jonathan yace banbancin Addini da Kabilanci na daga cikin abinda ke hana kasarnan ci gaba. Jonathan yace abin na damunsa kuma idan ba'a gyara ba, haka za'a ci gaba da tafiya har 'ya'ya da jikoki. Yace mafi yawancin matsalolin da muke fuskanta a kasarnan duk saboda wannan matsala ce ta nuna banbancin Addini da kabilanci. Jonathan yace a irin wannan tsari da wuya a samu shugaba na gari.
DA ƊUMI-ƊUMI: Wata budurwa ta fito kan titi dauke da allo inda take shaidawa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf cewa ta gama karatu amma ba aiki, ta ce harakar kwamfuta ta karanta amma duk aikin da aka bata tana so

DA ƊUMI-ƊUMI: Wata budurwa ta fito kan titi dauke da allo inda take shaidawa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf cewa ta gama karatu amma ba aiki, ta ce harakar kwamfuta ta karanta amma duk aikin da aka bata tana so

Duk Labarai
Wata budurwa ta fito kan titi dauke da allo inda take shaidawa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf cewa ta gama karatu amma ba aiki, ta ce harakar kwamfuta ta karanta amma duk aikin da aka bata tana so. Shin akwai ire-iren wannan budurwa da suka kammala karatu amma babu aikin yi a wajen ku? Wane fata kuke mata? Ta roki a taya ta yadawa (SHARING) ko Allah zai sa ta dace! Daga A Yau
Bidiyo: Kalli yanda wata yar Najeriya ke sharbar kuka bayan da aka hanata shiga kasar Amurka bayan an ga abinda ta rubuta a shafinta na sada zumunta

Bidiyo: Kalli yanda wata yar Najeriya ke sharbar kuka bayan da aka hanata shiga kasar Amurka bayan an ga abinda ta rubuta a shafinta na sada zumunta

Duk Labarai
Wata 'yar Najeriya ta bayar da labarin cewa an bata Visa ta shiga kasar Amurka. Amma a yayin bincike, bayan da aka ga abinda ta rubuta, an hanata shiga kasar. https://twitter.com/General_Somto/status/1939214048584736850?t=Pu6_fQVOawm3a8xsa59AeQ&s=19 Ta wallafa Bidiyo tana ta kuka hadda majina tana bayar da ba'asin yanda lamarin ya kasance.
Idan muka dage, Cikin shekaru 5 zamu iya maida Afrika Aljannar Duniya>>Inji Dangote

Idan muka dage, Cikin shekaru 5 zamu iya maida Afrika Aljannar Duniya>>Inji Dangote

Duk Labarai
Attajirin Najeriya, Aliko Dangote ya bayyana cewa, idan aka dage a Afrika, cikin shekaru 5 za'a iya mayar da nahiyar Aljannar Duniya. Ya bayyana hakane a wajan wata hira da aka yi dashi. Dangote ya bayyana cewa, babbar matsalarmu a Afrika shine satar kudi da ake ana kaiwa kasashen ketare. Yace babu inda ba'a rashawa da cin hanci, yace amma matsalar ta Africa shine, maimakon idan an sata a zuba jari da kudin a Afrika, sai a mayar dasu zuwa kasashen waje. Dangote yace ba wai yana karfafa satar kudin Gwamnati bane amma abinda yake cewa, shine a daina kai kudaden kasashen waje.
Sharudan da aka gindaya min kamin a mayar da ni Gwamna basu da dadi amma na amince>>Inji Fubara

Sharudan da aka gindaya min kamin a mayar da ni Gwamna basu da dadi amma na amince>>Inji Fubara

Duk Labarai
Dakataccen Gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara ya bayyana cewa, Sharudan da aka gindaya masa ya cika kamin a mayar dashi kan kujerar gwamna basu da dadi. Yace amma ya amince dasu. Fubara ya bayyana hakane a yayin ganawa da kungiyar masoyansa inda yace musu su amince da sharadin suma domin indai ba rayuwarsa aka ce ya bayar ba zai amince da duk wani sharadi dan dai a zauna lafiya. Fubara ya bayyana cewa, suna godiya da irin rawar da Wike ya taka wajan ci gaban jihar da kawo karshen rikicin jihar. Wasu daga cikin sharudan da aka gindayawa Fubara sune dole ya amince ba zai sake tsayawa takara a zaben shekarar 2027 ba sannan zai biya 'yan majalisar jihar hakkokinsu da ya dakatar, sannan Wike ne zai tsayar da 'yan takarar kananan hukumomi a jihar.
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda Paul Pogba ke kuka bayan Komawa kungiyar AS Monaco

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda Paul Pogba ke kuka bayan Komawa kungiyar AS Monaco

Duk Labarai
Paul Pogba ya saka hannun yarjejeniya da kungiyar AS Monaco. Zai bugawa kungiyar wasa na tsawon shekaru 2 zuwa shekarar 2027. Hakan na zuwane bayan da ya kammala dakatarwar shekaru 2 da aka masa bayan samunshi da ta'ammuli da miyagun kwayoyi. https://twitter.com/NigeriaStories/status/1939052855815741547?t=K6H25L7HO2F_6YNje1ZAIA&s=19 Da farko an yanke masa dakatarwar shekaru 4 amma daga baya aka mayar dashi shekaru 2 bayan ya daukaka kara. Saidai Pogba a yayin da yake sakawa AS Monaco hannu ya fashe da kuka inda aka rika bashi baki.
Bidiyo: Mansurah Isah ta bayyana yanda ta tsira daga hannun ‘yan damfara

Bidiyo: Mansurah Isah ta bayyana yanda ta tsira daga hannun ‘yan damfara

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana yanda ta tsira daga hannun 'yan Damfara. Mansurah tace wani yaro ya je gidanta inda ya rubuta sunanta a jikinsa da sunan cewa, wai yana sonta, yana son ta taimaka masa. Saidai tace ta kai maganar wajan 'yansanda inda aka mayar da yaron Bauchi saboda yace daga kauyen Bauchi ya fito, tace ta yi yunkurin tallafawa yaron inda tace a tambayo kudin makarantar Bokonsa da Arabi. Tace amma sai akance wai makarantar Arabi ana biyan Naira dubu 70 duk wata ita kuma Boko ana biyan Dubu 150 duk wata. Mansurah tace data ga abin nasu damfara ne sai kawai ta ce a bar maganar ta daina kulasu. Tace kwatsam sai gashi kuma ta ga yaron wai ya rubuta sunan Lilin Baba a jikinsa. Mansurah tace Allah ya ceceta. Kalli Bidiyon ta: https://...