Tuesday, March 3
Shadow

Duk Labarai

Da Duminsa: Jam’iyyar NNPP ta Lashe zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono

Da Duminsa: Jam’iyyar NNPP ta Lashe zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono

Duk Labarai
Jam'iyyar NNPP ta Lashe zaben cike gurbi na Bagwai da Shanono da aka gudanar jiya, Asabar a Kano. Da yake bayyana sakamakon zaben da misalin karfe  12:36am na safe, Professor Hassan Shitu ya bayyana dan takarar NNPP, Dr Ali Kiyawa a matsayin wanda ya lashe zaben da kuri'u 16,198 inda ya kayar da dan takarar APC, Ahmad Kadamu, da ya samu kuri'u 5,347. 'Yan Jam'iyyar NNPP sun gudanar da zaman dirshan a ofishin INEC inda suka zargi cewa, ana shirin yin murdiyar zabe a sakamakon mazabar Ghari/Tsanyawa. Kakakin Gwamnatin jihar Kano, Sanusi Tofa yace ba zasu bar kofar INEC din ba sai an fadi sakamakon Ghari/Tsanyawa
EFCC ta kwato Naira Biliyan 5 da dala Miliyan $10 daga hannun barayin tsaffin ma’aikatan NNPCL

EFCC ta kwato Naira Biliyan 5 da dala Miliyan $10 daga hannun barayin tsaffin ma’aikatan NNPCL

Duk Labarai
Hukumar hana rashawa da cin hanci, EFCC ta kwato Naira Biliyan 5 da Dala Miliyan $10 daga hannun tsaffin ma'aikatan NNPCL da 'yan Kwangila. Wadannan kudade na da alaka da gyaran matatun man Kaduna, Fatakwal, da Warri. Hakanan kuma Punchng tace ta samu karin bayanin cewa, EFCC din na kokarin kara kwato wasu Naira Biliyan 10 da wasu dala Miliyan $13 da suma aka karkatar dasu. Rahoton yace shugaban EFCC, Ola Olukoyede da kansa ne ke jagorantar wannan bincike musamman ganin yanda aka kashe makudan kudade wajan gyaran matatun man Najeriya amma har yanzu basa aiki. Gwamnatoci da suka shude sun yi kokarin gyaran matatun man fetur din amma basu yi nasara ba.
Kalli Bidiyo: An Kama Akwatin Zaɓe Da Na’urar BVAS A Motar Jigon APC, Mustapha Salihu, A Zaben Ganye

Kalli Bidiyo: An Kama Akwatin Zaɓe Da Na’urar BVAS A Motar Jigon APC, Mustapha Salihu, A Zaben Ganye

Duk Labarai
An Kama Akwatin Zaɓe Da Na’urar BVAS A Motar Jigon APC, Mustapha Salihu, A Zaben Ganye. Wasu jami’an tsaro a jihar Adamawa sun gano akwatin zaɓe da na’urar tantance masu kada kuri’a (BVAS) a cikin motar Mustapha Salihu, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa (Arewa maso Gabas), yayin gudanar da zaben cike gurbi a mazabar Ganye. Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan siyasa da jama’a, inda ake zargin yunkuri ne na murde sakamakon zaɓe. An ce an kama kayan zaɓen ne yayin da ake gudanar da aikin tantance kuri’u a wasu rumfunan zaɓe, kuma hakan ya janyo tarin mutane da bacin rai. Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da hukumomin tsaro har yanzu ba su fitar da cikakken bayani kan lamarin ba, amma al’ummar yankin da dama na bukatar a gudanar da bincike tare da daukar ...
Har Gida Shugaban Kasar Libiya Ya Ziyarci Daliba ‘Yar Asalin Kasarsa, Bayan Ta Zo Na Daya A Gasar Adabin Larabci Na Duniya Domin Karrama Ta

Har Gida Shugaban Kasar Libiya Ya Ziyarci Daliba ‘Yar Asalin Kasarsa, Bayan Ta Zo Na Daya A Gasar Adabin Larabci Na Duniya Domin Karrama Ta

Duk Labarai
ALLAH DAYA GARI BANBAM: Har Gida Shugaban Kasar Libiya Ya Ziyarci Daliba 'Yar Asalin Kasarsa, Bayan Ta Zo Na Daya A Gasar Adabin Larabci Na Duniya Domin Karrama Ta Da yake kasar tana da kishin dalibanta, shugaban kasa Abdul Hanid da kansa ya kaiwa dalibar mai suna Nadia ziyara har gida don karrama ta. Wannan labari na dauke da darasi mai yawa game sa shugabanninmu na Nijeriya.
Gwamnatin Najeriya za ta kashe biliyan N13 don inganta lantarki a sashen jihar Legas

Gwamnatin Najeriya za ta kashe biliyan N13 don inganta lantarki a sashen jihar Legas

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta amince da ware biliyoyin naira domin gyarawa da kuma inganta hanyoyin samar da lantarki a faɗin ƙasar, ciki har da naira biliyan 13 da za a kashe a jihohin Legas da Ogun. Ministan Lantarki Adebayo Adelabu ya faɗa jim kaɗan bayan kammala zaman majalisar zartarwa ranar Laraba cewa sun amince da daftari huɗu domin inganta ɓangaren samar da lantarkin ƙasar. Daftari na farko, in ji ministan, shi ne cigaba da biyan diyya ga mutanen da aka karɓi gine-gine ko kadarorinsu domin yin aikin isar da layukan lantarki ta wurin. "Majalisa ta amince da biyan diyyar naira biliyan 13 a ƙarƙashin kamfanin lantarki na Lagos Transmission Industrial Project, wanda za a biya da bashin dala miliyan 238 da bankin Japan International Cooperation Agency (JICA) zai bayar," a cewarsa. ...
Tinubu ya amince da biliyan 16 don sake gina gadar Mokwa – Mohammed Idris

Tinubu ya amince da biliyan 16 don sake gina gadar Mokwa – Mohammed Idris

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da kashe naira biliyan 16.7 domin sake gina gadar Mokwa da ke jihar Neja a tsakiyar ƙasar, wadda ambaliya ta lalata. Ministan Yaɗa Labarai Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a yau Asabar, yayin da shi kuma Ministan Ayyuka David Umahi ya ce shugaban ya amince da yin irin wannan aiki a jihohi da dama. "Muna godiya ga shugaban ƙasa da minista [na ayyuka]. Tattaunawa kawai muka yi da shi kafin mu je wajen shugaban ƙasa, wanda shi kuma ya amince. Abu ne mai muhimmanci ga al'umma," a cewar Idris. Umahi ya ce sauran jihohin da za a yi aikin sun ƙunshi gadar Wukari a jihar Taraba, da gadar Lokoja a jihar Kogi, da gadar Afikpo a jihar Ebonyi, da gadar sama ta Keffi a jihar Nasarawa, da gadar Jebba a Kwara, da gadoji bakwai a jihar Edo, da kuma wata g...
A soke zaben cike gurbi na Kano, Bamu yadda dashi ba>>Inji Jam’iyyar APC

A soke zaben cike gurbi na Kano, Bamu yadda dashi ba>>Inji Jam’iyyar APC

Duk Labarai
Jam'iyyar APC ta bayyana cewa, bata yadda da zaben cike gurbi na Kano ba inda tace INEC ta sokeshi da gaggawa. Sakataren yada labarai na jam'iyyar, Felix Morka ne ya bayyana hakan a Abuja ranar Asabar inda yace suna kira ga INEC ta soke zaben da gaggawa. Yayi zargin cewa, 'yan Bangar siyasa a Shanono da Bagwai da Ghari sun tayar da hankula sosai ta hanyar amfani da muggan makamai. Yace masu zabe dole suka tsere inda suka sha karfin jami'an tsaron da aka kai wajan wanda hakan yasa zabe me inganci ba zai samu ba.