Sunday, April 19
Shadow

Matar Tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta bayyana kayan aikinta da ICPC suka dauka da suka je bincike gidan mijinta wanda a tunaninsu shine na’urar yiwa waya kutse

Matar tsohon Gwamnan Kaduna, Hajiya Hadiza Ismail El-Rufai ta wallafa a shafinta cewa, ICPC sun dauke mata na’urar da take amfani da ita a banki.

Tace tana rantsuwa da Allah na’urar ba ta kutsen waya bace.

Ta bayyana cewa, cikin kayan da ICPC suka bayyana cewa sun dauka daga gidan Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, sun manta su bayyana wannan na’urar tata.

ICPC dai sun bayyana wayoyi da kwamfutocin tafi da gidanka a matsayin abubuwan da suka gano a gidan malam Nasiru Ahmad El-Rufai.

Karanta Wannan  Kalli, Anata Allah Wadai da mawaki Bilal Villah bayan da ya je Ka'aba ya daga Wakar da yayi da Naziru Sarkin Waka, yana rokon Allah ya sa mata Albarka

A baya kuma sun zargi cewa, sun gani na’urar yiwa waya kutse.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *