Monday, December 15
Shadow

Duk Labarai

Bidiyo: Ba haka ake aiki ba, wannan zubar da mutunci ne>>Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi Allah wadai da yanda wasu ‘yansanda suka yiwa wata jarumar fina-finan kudu da ta yi shigar banza rakiya

Bidiyo: Ba haka ake aiki ba, wannan zubar da mutunci ne>>Hukumar ‘yansandan Najeriya ta yi Allah wadai da yanda wasu ‘yansanda suka yiwa wata jarumar fina-finan kudu da ta yi shigar banza rakiya

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya ta nuna rashin jin dadinta game da abinda wasu jami'anta suka aikata na yiwa jarumar fina-finan kudu, Angela Okorie rakiya yayin da take sanye da shigar banza take gudu. Bidiyon nata ya watsu sosai a kafafen sada sumunta wanda hakan ya jawo cece-kuce. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1933204045562581459?t=O4C3uPPz_0kZM96RndY-lg&s=19 Dan haka hukumar 'yansandan ta fitar da sanarwar cewa abinda 'yansandan suka aikata baya cikin tsarin aikin dansanda. Hukumar tace tana kan Bincike kuma zata dauki matakin da ya dace bayan kammala binciken lamarin.
Kalli Bidiyo: A baibul an gaya mana cewa dolene Miji ya tabbatar yana biyawa matarsa bukatar Jìmà’ì, idan ba haka ba, zata iya cin amanarsa>>Inji Wannan Matar

Kalli Bidiyo: A baibul an gaya mana cewa dolene Miji ya tabbatar yana biyawa matarsa bukatar Jìmà’ì, idan ba haka ba, zata iya cin amanarsa>>Inji Wannan Matar

Duk Labarai
Wannan matar ta bayyana cewa, a baibul an gayawa mazaje au biyawa matansu bukatar Jima'i dan kaucewa cin amana. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1937827279239098637?t=A0DINMbjdxhjB2h3J5Dthg&s=19 Ta bayyana cewa, kuma jikin mace an ce musu ba nata bane, na mijinta ne hakanan shima namijin ba nasa bane na matarsa ne.
Ni ne gatan ‘yan Najeriya, Duk wani da zai zo ya ce muku zau kayar dani zabe a 2027 kada ku saurareshi>>Shugaba Tinubu

Ni ne gatan ‘yan Najeriya, Duk wani da zai zo ya ce muku zau kayar dani zabe a 2027 kada ku saurareshi>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatinsa ce gatan 'yan Najeriya inda yace kada su saurari masu cewa zasu kayar dashi zabe a 2027. Shugaban yace 'yan adawar dake hada kai da zummar kayar dashi zabe 'yan gudun hijirar siyasa ne. Shugaban ya bayyana hakane ranar Laraba a yayin ziyarar da ya kai jihar Nasarawa ta kwana daya. Ya yabawa gwamnan jihar, Abdullahi Sule kan aikin da yakewa mutanen jiharsa inda yace zai tallafa masa da dukkan wani aikin ci gaba da zai kawo.
A yau shugaba Tinubu zai sakawa sabbin dokokin Haraji hannu

A yau shugaba Tinubu zai sakawa sabbin dokokin Haraji hannu

Duk Labarai
A yau, Alhamis ne ake sa ran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai sakawa sabbin kudirin dokokin Haraji hannu a fadarsa dake Abuja. Hakan na kunshene cikin sanarwar da kakakin shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar. Kudirin dokokin guda 4 ne wanda tuni majalisar tarayya ta amince dasu bayan cece-kuce da suka jawo sosai. Shuwagabannin majalisar tarayya da shuwagabannin kungiyoyin gwamnoni da ministan kudi da sauran manyan ma'aikatan Gwamnati ne zasu shaida wannan lamari a fadar shugaban kasar kamar yanda sanarwar ta tabbatar.
TIRƘASHI: Ba zan goyi bayan Tinubu ba idan ya sauke Shettima – Sheikh Jingir

TIRƘASHI: Ba zan goyi bayan Tinubu ba idan ya sauke Shettima – Sheikh Jingir

Duk Labarai
TIRƘASHI: Ba zan goyi bayan Tinubu ba idan ya sauke Shettima – Sheikh Jingir. Fitaccen Malamin Addinin Musulunci a Nijeriya Sheikh Sani Yahaya Jingir, ya ce ba zai goyi bayan Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 ba, idan har Tinubu ya sauya mataimakinsa, Kashim Shettima. Jingir ya bayyana cewa matsayar shi ita ce goyon baya ga Tinubu–Shettima ne kawai. Idan Tinubu ya yanke shawarar sauya Shettima da wani daga cikin mataimakinsa.
Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga Yuni, 2025, a matsayin hutu domin shiga Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447 Hijira.

Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga Yuni, 2025, a matsayin hutu domin shiga Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447 Hijira.

Duk Labarai
Gwamnatin Jihar Kano ta ayyana gobe Alhamis, 26 ga Yuni, 2025, a matsayin hutu domin shiga Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1447 Hijira. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma taya al’ummar Musulmi murna bisa samun damar ganin sabuwar shekarar, wadda ke farawa da watan Muharram – watan farko a kalandar Musulunci ta hijira. Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya fitar a yau Laraba. Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da kuma Musulmi gaba ɗaya da su yi duba kan ayyukansu na shekarar da ta gabata, tare da amfani da wannan dama domin yin addu’o’i na zaman lafiya, haɗin kai da cigaba a jihar da kuma ƙasa baki ɗaya.
Shugaba Tinubu ya amince da kafa makarantar nakasassu da asibitin kashi a jihar Gombe

Shugaba Tinubu ya amince da kafa makarantar nakasassu da asibitin kashi a jihar Gombe

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince da kudirin dokoki 2 na kafa makarantar nakasassu da kuma asibitin kashi a jihar Gombe. Majalisar Dattijai ta jinjinawa shugaban kasan kan wannan yunkuri wanda tace zai habbaka harkar ilimi da kiwon lafiya. Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ne ya bayyana haka a yayin zaman majalisar Dattijai na ranar Laraba. Za'a gina makarantar nakasassun ne a karamar hukumar Dukku dake jihar.