Wednesday, March 4
Shadow

Duk Labarai

Yau wata guda kenan daidai da rashin shugaba Buhari, har yanzu ina jin zafin rashinsa, ji nake kamar yau ya rasu>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Yau wata guda kenan daidai da rashin shugaba Buhari, har yanzu ina jin zafin rashinsa, ji nake kamar yau ya rasu>>Inji Tsohon Hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad

Duk Labarai
Tsohon hadimin shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya bayyana alhinin tsohon shugaban kasa, Marigayi Muhammadu Buhari. Ya bayyana cewa, wata guda kenan da rasuwar shugaba Buhari inda yace Buhari ya kafa tarihi da rayuwa me nagarda wadda zata dawwama ana tunawa da ita. Ya bayyana cewa har yanzu zafin rashin Buhari bai gushe a zuciyarsa na dan ji yake kamar yaune Buharin ya rasu.
Gidana na Alfarma da ake ta cece-kuce akai na ginashi ne tun kamin in zama Minista>>Inji Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu

Gidana na Alfarma da ake ta cece-kuce akai na ginashi ne tun kamin in zama Minista>>Inji Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu

Duk Labarai
Ministan Wutar Lantarki, Adebayo Adelabu yayi martani kan rahotannin dake cewa ya gina gidansa ne a shekaru biyu bayan da ya zama Minista. Da yake magana ta bakin me magana da yawunsa, Mr. Femi Awogboro, Ministan yace maganar gaskiya ya kammala ginin gidanne a shekarar 2023, wata daya kamin a nadashi minista. Ministan ya kuma nuna hotuna a matsayin shaidar ikirarinsa inda yayi kiran cewa, tun kamin ya hau mukamin Minista ya gina gidan. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1955311072488964410?t=PdwSmz3RpdaUYga-kyaqdA&s=19 An dai rika tambayar ina ya samu kudin gina katafaren gida haka shekaru 2 kacal da zamansa minista?
Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda ‘yan Najeriya suka shiga damuwa sosai bayan ganin kakakin majalisa, Godswill Akpabio yana tafiya da kyar yana dogara sanda

Allah Sarki: Kalli Bidiyon yanda ‘yan Najeriya suka shiga damuwa sosai bayan ganin kakakin majalisa, Godswill Akpabio yana tafiya da kyar yana dogara sanda

Duk Labarai
An hango kakakin majalisar dattijai, Sanata Godswill Akpabio yana tafiya da kyar yana dogara sanda bisa rakiyar mukarrabansa. https://twitter.com/ChuksEricE/status/1955311072488964410?t=e_v88sFvmeE81bjCbMAz4g&s=19 Wasu dai sun rika cewa tsufa ne ke damunsa. A baya dai an rika yada rade-radin cewa bashi da lafiya.
Muna Magana da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aiki yi a wadannan kasashe>>Gwamnatin Tarayya

Muna Magana da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aiki yi a wadannan kasashe>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, suna aiki tare da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aikin yi a wadannan kasashe. Ministan Gwadago, Muhammad Dingyadi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja. Yace suna horas da matasan wanda zasu je wadannan kasashe su yi aiki kuma abin ya amfane su da kasa baki daya. Ministan yace yanzu haka suna magana da daya daga cikin kasashen kuma sauran kasashen ma zasu ci gaba da neman wa matasan aikin a can.
Kalli Bidiyon yanda Ministan Wutar Lantarki ke nuna katafaren gidan daya gina yana Alfahari dashi

Kalli Bidiyon yanda Ministan Wutar Lantarki ke nuna katafaren gidan daya gina yana Alfahari dashi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Ministan Wutar Lantarkin, Adeboye Adelabu na ci gaba da shan caccaka saboda katafaren gidan da ya nuna wanda ya gina. Ya gina gidanne a Ibadan jihar Oyo inda aka ganshi a Bidiyon yana Alfahari da hakan. Da yawa dai sun rika tambayar ina ya samu kudin gina gida irin wannan a dan kankanin lokacin da yayi a matsayin minista? https://twitter.com/ChuksEricE/status/1955023808819233232?t=lPssTdurdmZH1IEhU8Sw6A&s=19
Kalli Bidiyo: Matashi Garba Maiwada ya zargi Gwamna Zulum da yin dama-dama da Maiduguri ta yanda matasa sai tafiya ci rani suke saboda ba aikin yi a garin

Kalli Bidiyo: Matashi Garba Maiwada ya zargi Gwamna Zulum da yin dama-dama da Maiduguri ta yanda matasa sai tafiya ci rani suke saboda ba aikin yi a garin

Duk Labarai
Matashi Garba Maiwada ya gayawa gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum cewa, sun yi dama-dama da garin Maiduguri ta yanda garin a yanzu babu aikin yi. Matashin yace amma na kusa da gwamnan basa gaya masa gaskiya Matashin yace ba zasu zabi wani ba wai dan Gwamna Zulum yace a zabeshi, yace ko da kuwa Gwamna Zulum dinne a yanzu ya dawo ba zasu sake zabenshi ba. https://www.tiktok.com/@garbamaidawa/video/7536889948037795128?_t=ZS-8yq7YYqADTN&_r=1
Kalli Bidiyo: Mutane basa yawo shiyasa suke mamaki dan nace an bani kwangilar Biliyan 4 suna ganin karyane, Ni kuma ina yawo, ba kasuwancin da bana yi kuma yanzu haka an sake bani gidajen Naira Biliyan 5 in sayar>>Mansurah Isa

Kalli Bidiyo: Mutane basa yawo shiyasa suke mamaki dan nace an bani kwangilar Biliyan 4 suna ganin karyane, Ni kuma ina yawo, ba kasuwancin da bana yi kuma yanzu haka an sake bani gidajen Naira Biliyan 5 in sayar>>Mansurah Isa

Duk Labarai
Tauraruwar fina-finan Hausa, Mansurah Isah ta bayyana cewa, mutane na mamakin tace an bata kwangilar Naira Biliyan 4. Tace abinda da yawa basu fahimta ba shine, ba wai Biliyan 4 tsabar kudi ake magana ba, ana maganar a rubucene. Tace idan tsabar kudi ake magana, ko Dangote da me kudin Duniya, Elon Musk basu taba ganin Biliyan 4 a zahiri ba duk yawanci a takarda ne. Tace kuma matsalar mutane basa yawo ne shiyasa, tace amma ita tana yawo kuma ita 'yar kasuwa ce dan haka ko a yanzu ma an bata gidajen Naira Biliyan 5 ta sayar a Abuja. https://www.tiktok.com/@nassxee_hausa_tv/video/7536705865944993080?_t=ZS-8ypznj1pQCf&_r=1
Kotu ta cewa Gwamnatin tarayya ta kawo karshen Shari’ar Dasuki

Kotu ta cewa Gwamnatin tarayya ta kawo karshen Shari’ar Dasuki

Duk Labarai
Kotu ta ba gwamnatin tarayya wa’adin Satumba kan shari’ar Dasuki. Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adin zuwa ranakun 24, 25 da 26 ga watan Satumba domin kammala shari’ar tsohon mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro , Kanal Sambo Dasuki (mai ritaya), kan zargin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba da badakalar kudi. Mai shari’a Peter Lifu ya umurci gwamnati ta kammala kiran shaidu da gabatar da dukkan shaidun da za ta dogara da su a shari’ar da ta fara tun 2015. A zaman baya, kotu ta karbi kayayyakin da aka samo daga gidajen Dasuki a Abuja da Sokoto a matsayin shaida, ciki har da kwamfuta, wayoyi, kudi da takardun banki. An dage shari’ar zuwa Satumba domin gwamnati ta rufe gabatar da shaidu sannan Dasuki ya fara kare kansa....
Kalli Bidiyo: Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) baya cutarwa baya amfanarwa, yana Kabari, Kuma duk me neman ya bashi wani abu ba zai samu ba, ka nema a wajan Allah>>Inji Malam Abdurrahman Umar

Kalli Bidiyo: Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) baya cutarwa baya amfanarwa, yana Kabari, Kuma duk me neman ya bashi wani abu ba zai samu ba, ka nema a wajan Allah>>Inji Malam Abdurrahman Umar

Duk Labarai
Malam Abdurrahman Umar ya gargadi masu neman wani abu a wajan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa, zasu mutu basu samu ba dan Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) yana kabari, baya cutarwa baya amfanarwa. Ya bayyana hakane a wani wa'azinsa daya yadu sosai. Yace Suffar Allah ce ake jinginawa ga Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) https://www.tiktok.com/@abdurrahmanumarr/video/7537055471803403576?_t=ZS-8ypuAvQiki1&_r=1