Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan ya kaiwa shugaban jam'iyyar ADC, David Mark ziyara a gidansa dake Abuja.
Rahotanni sun ce sun tattauna muhimman batutuwa.
Wannan ziyara tasa dai ta jawo muhawa me zafi.
Rahama Saidu me babban shago ta dauki hankula inda ta mikawa daya daga cikin kwatomominta hannu su gaisa amma yaki yadda ya mika mata hannu.
Inda a gefe daya kuma ta mikawa Soja Boy hannu suka gaisa.
Lamarin ya jawo cece-kuce inda wasu ke cewa wai Namiji ne yake kin shan hannun mace amma ita tana mika masa hannu.
A baya dai Soja Boy da Rahama Saidu sun gaisa hakanan ya ma rungumeta lamarin da ya jawo cece-kuce me zafi.
https://www.tiktok.com/@abu_ayrin_backup/video/7553946644190989575?_t=ZS-9029A5Isqh7&_r=1
Tauraron Tiktok, Bashir Gombe ya bayyana cewa, ya je kasar waje karbo iPhone kamar yanda ake yi amma abinda aka ce za'a yi dashine yaki amincewa saboda abin yayi Muni.
Kalli Bidiyon jawabinsa a kasa:
https://www.tiktok.com/@bashirgombe76/video/7552563168225070354?_t=ZS-9026tA94XJ2&_r=1
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya gargadi kiristoci masu son tafiya jeru salem Ibada cewa kada wanda ya makale a can yaki dawowa Najeriya.
Shugaban yace babu kasar data kai Najeriya 'yanci da dadi musamman idan mutum na zaune a wata kasar ba bisa ka'ida ba.
Shugaban ya bayyana hakane ta bakin Sakataren Gwamnatin tarayya, Sanata George Akume a yayin da kiristocin ke shirin tafiya aikin ibadar.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa, ba gaskiya bane labarin da yake yawo cewa wai yace zai baiwa yarbawa kulawa da mukamai na musamman idan ya zama shugaban kasa.
Atiku yace wanda ya fitar da sanarwar da yawunsa me suna Kola Johnson be sanshi ba.
Atiku ya bayyana hakane ta bakin me magana da yawunsa Paul Ibe.
Inda ya bukaci a yi watsi da wannan magana.
Matashiyar nan marar kunya ta jihar Legas, Ayomiposi Oluwadahunsi wadda aka fi sani da Mandy Kiss tace duk da kundin tarihin Duniya yace ba zai karrama ta ba idan ta yi lalata da maza 100, ba zata fasa ba.
Tace tuni ta sayi fakiti na kwandam inda take gayyatar maza zuwa Ikorodu.
Tace ko da mutum ba zai yi ba, tana gayyatarsa ya je ya sha kallo.
Ta bayyana cewa dai a watan Oktoba ne zata aikata wannan masha'a saidai bata fadi sunan wajan da zata aikata hakan ba.
https://twitter.com/Teeniiola/status/1970723550521893060?t=_QdTAUIMpixvtqGHkHOeLA&s=19
https://twitter.com/Teeniiola/status/1971143834601132165?t=1bukeNydE-hM6KU_yjWQ1g&s=19
Rahotanni sun ce har yanzu gidajen man fetur na sayar da man a farashi me tsada duk da rage farashin da matatar man fetur ta Dangote ta yi.
A makon daya gabata ne Matatar man ta sanar da rage farashin daga Naita 865 zuwa naira 820 akan kowace lita musamman tace saboda tankokin man ta 1000 zasu fara jigilar man zuwa gidajen mai kyauta.
Saidai binciken da jaridar Punchng ta yi yace har yanzu a jihohin Legas da Ogun da sauran wasu jihohi gidajen man basu fara sayar da man a sabon farashi ba.
Tauraruwar Tiktok, Rahama Sa'idu ta bayyana cewa, Wannan jakar farashinta Naira 105,000 ne a shagonta.
Ta bayyana hakane a wani Bidiyonta da ya karade kafafen sadarwa inda lamarin ya baiwa mutane mamaki musamman kanin jikar karamace sosai.
Kalli Bidiyon anan
Wannan amaryar daga jihar Bauchi me suna shahida Sani ta amince da Qur'ani a matsayin sadakinta maimakok kudi da aka saba bayarwa.
An daura aurenta da angonta, Aliyu Haidar ranar Asabar data gabata a unguwar Saleh Saleh dake jihar Bauchi.
Lamarin ya dauki hankula inda akaita muhawa da kuma yabawa saukin kan amaryar