Saturday, December 13
Shadow

Duk Labarai

Tsohon soja ya mùtù a hannun ‘Yàn Bìndìgà duk da biyan Naira Miliyan 10 a matsayin kudin fansa

Tsohon soja ya mùtù a hannun ‘Yàn Bìndìgà duk da biyan Naira Miliyan 10 a matsayin kudin fansa

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Kogi na cewa, wani tsohon soja me suna Major Joe Ajayi ya rasu a hannun masu garkuwa da mutane duk da danginsa sun biya kudin fansarsa Naira Miliyan 10. An yi garkuwa dashine a gidansa dake Odo-Ape na karamar hukumar Kabba-Bunu ranar May 21, 2025 da misalin karfe 11:30pm. Da farko dai wanda suka yi garkuwa dashi sun nemi Naira Miliyan 50 inda daga baya da suka ga bashi da lafiya zai rasu. Sai suka ce a kai musu Naira Miliyan 10, bayan da aka kai musu, suka bayyana inda za'a je a daukeshi, sai gawarsa aka tarar. Tuni aka kai gawar tasa zuwa mutuware dake Asibitin Kabba Specialist Hospital. Masu garkuwa da mutane sun matsawa jihar Kogi a 'yan kwanakinnan.
Ya Zama Wajibi Ga Ƴan Nijeriya Mu Tashi Tsaye Wajen Ganin An Kawar Da Gwamnatin APC 2027 A Kowane Matakai, Saboda Mawuyacin Halin Da Ta Jefa Mu, Ta Hanyar Haɗaka Da Muke Shirin Kafawa Nan Gaba Kaɗan, Cewar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa

Ya Zama Wajibi Ga Ƴan Nijeriya Mu Tashi Tsaye Wajen Ganin An Kawar Da Gwamnatin APC 2027 A Kowane Matakai, Saboda Mawuyacin Halin Da Ta Jefa Mu, Ta Hanyar Haɗaka Da Muke Shirin Kafawa Nan Gaba Kaɗan, Cewar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa

Duk Labarai
Ya Zama Wajibi Ga Ƴan Nijeriya Mu Tashi Tsaye Wajen Ganin An Kawar Da Gwamnatin APC 2027 A Kowane Matakai, Saboda Mawuyacin Halin Da Ta Jefa Mu, Ta Hanyar Haɗaka Da Muke Shirin Kafawa Nan Gaba Kaɗan, Cewar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Dakta Mustapha Inuwa Daga Jamilu Dabawa, Katsina
Kalli Bidiyo: Ya yi hàdàrì da motarsa jim kadan bayan da ya sayota daga wajan sayar da mota

Kalli Bidiyo: Ya yi hàdàrì da motarsa jim kadan bayan da ya sayota daga wajan sayar da mota

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false,"used_sources":{"version":1,"sources":[{"id":"336487999083211","type":"ugc"}]}} Wannan wani matashi ne da ya sayo sabuwar mota, saboda doki ya rika gudun wuce sa'a da ita har daga karshe ya je ya fada cikin wani gini. https://twitter.com/General_Somto/status/1932040367978795216?t=YNBNkpoFUVPDxlF7qYnYNQ&s=19 Wasu dai sun jajanta masa inda wasu suka mai Allah kara.
Kalli Hotuna yanda aka gano Kòkòn kàn mùtùm a cocin wani fasto da ake zargi da yin tsàfì da sàssàn jìkìn mutane

Kalli Hotuna yanda aka gano Kòkòn kàn mùtùm a cocin wani fasto da ake zargi da yin tsàfì da sàssàn jìkìn mutane

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Enugu sun sanar da gano kokon kan mutum a wani kango inda aka ginin wata coci. Ana zargin faston cocin da ake kira da Chinedu Solomon Ezedike yana amfani da sassan jikin dan Adam wajan gudanar da tsafi. An gano hakan ne bayan binciken hadaka wanda aka yi da DPO din 'yansanda na karamar hukumar Igbo-Eze dake jihar. A baya dai an zargi faston da kashe wasu mutane 4 'yan uwan juna wanda ake zargin yayi amfani dasu ne wajan aikata tsafi. Shugaban karamar hukumar, Barrister Ferdinand Ukwueze ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace jami'an tsaro sun kai samame wajanne bayan samun bayanan sirri. Rahoton yace ana kan ci gaba da binciken lamarin.
Gwamnatin Tarayya zata farfado da kamfanin Karafa na Ajakuta

Gwamnatin Tarayya zata farfado da kamfanin Karafa na Ajakuta

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya zata korkiro da kamfanin Karafa na Ajakuta. Ministan karafa, Shuaibu Abubakar Audu, ne ya bayyana hakan inda yace Gwamnatin tuni ta shiga mataki na gaba wajan farfado da kamfanin. Ministan ya bayyana hakane a yayin da yake ganawa da wasu 'yan jam'iyyar APC yayin da suka kai masa ziyara a gidansa dake jihar Kogi. Yace tuni Gwamnatin ta shiga yarjejeniya dan farfado da kamfanin sannan tana kokarin jawo hankalin masu zuba hannun Jari musamman daga kasar China dan su zo su zuba jari a kamfanin dan farfado dashi. Yace suna aiki me kyau kan lamarin kuma zasu tabbatar sun bayar da sakamako me kyau.
Ali Nuhu ya dauki nauyin kula da Adam A. Zango bayan mummunan hadarin motar da yayi

Ali Nuhu ya dauki nauyin kula da Adam A. Zango bayan mummunan hadarin motar da yayi

Duk Labarai
RASHIN TAUSAYI:Ana zargin an sace wayar Adam A. Zango bayan ya yi haɗarin Mota. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wasu rahotanni sun nuna cewa Fitaccen Jarumin Kannywood Adam A. Zango ya rasa ɗaya daga cikin wayoyinsa ƙirar (Samsung) tare da kuɗi, biyo bayan sun samu haɗarin Mota a hanyar Kaduna zuwa Kano. Haɗarin wanda ya faru a ranar Lahadi, wanda tuni jarumin ya samu kulawa daga likitoci. Hakanan hadda cincin din da mahaifiyarsa ta bashi an sace. Wasu rahotanni sun ce Ali Nuhu ne ya dauki nauyin hidima d...
Matan Jihar Bayelsa sun bayyana takaici da watsi da Shugaba Tinubu yayi dasu bayan da suka masa yakin neman zabe

Matan Jihar Bayelsa sun bayyana takaici da watsi da Shugaba Tinubu yayi dasu bayan da suka masa yakin neman zabe

Duk Labarai
Mata magoya bayan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun bayyana takaici da jin Haushin watsi da aka yi dasu bayan da sukawa shugaban kasar yakin neman zabe. Matan sun nemi a sakasu cikin bayar da mukamin da shugaban kasar yake yi. Matan wadanda suka fito daga jihar Bayelsa sun bayyana hakane ta bakin wakiliyarsu a Abuja ranar Litinin. Tace a cikinsu akwai kwararrun mata da zasu taimaka wajan cimma muradun gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu idan aka basu dama. Ta bayyana takaicin yanda aka rasa mata a mukaman siyasa a Gwamnatin Tinubu duk da rawar da suka taka wajan yakin neman zabensa.
Kalli Bidiyo: Yanda shugaban kasar Amurka, Donald Trump yayi Tuntube ya kusa faduwa a yayin da yake hawa jirgin sama

Kalli Bidiyo: Yanda shugaban kasar Amurka, Donald Trump yayi Tuntube ya kusa faduwa a yayin da yake hawa jirgin sama

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi Tuntube inda ya kusa faduwa yayin da yake hawa matakalar jigin saman sa na Airforce One. Irin wannan lamari ya taba faruwa da tsohon shugaban kasar, Joe Biden inda akai ta masa tsiya da cewa tsufa ne ya masa yawa. https://twitter.com/LeadingReport/status/1931816469962035526?t=s7R7IHw5jPP7_Jz_id6weQ&s=19 Yanzu dai 'yan jam'iyyar Republicans dole bakinsu zai kulle saboda sune dama ke sukar Biden saboda hakan.
Tsohon Shugaban Sojoji, Janar Buratai yayi magana game da rahoton kai masa hàrì

Tsohon Shugaban Sojoji, Janar Buratai yayi magana game da rahoton kai masa hàrì

Duk Labarai
Tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Yusuf Tukur Burataiya musanta rahoton dake cewa an kai masa hari ya sha da kyar. A baya dai an ruwaito Sanata Ali Ndume yana cewa An kaiwa Buratai hari, saidai daga baya yace yana nufin garin Buratai ne ba tsohon shugaban sojojin ba. Buratai a sanarwar da ya fitar yace a Abuja yayi bikin Sallah tare da iyalinsa da 'yan uwa da abokan arziki. Yace maganar an kai masa hari bata da tushe ballantana makama inda yace ayi watsi da labarin. Yace yana godiya ga wadanda suka kirashi dan jin halin da yake ciki bayan samun wannan labari.
Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani

Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani. A wani labarin kuma an bayyana Ali nuhu ya taka rawar gani wajen ɗaukar nauyin kula da lafiyar sa.