Sunday, December 21
Shadow

Duk Labarai

Iyalan Mafarautan Da Aka Kàshè A Edo Sun Yi Zanga-zangar Neman Diyya

Iyalan Mafarautan Da Aka Kàshè A Edo Sun Yi Zanga-zangar Neman Diyya

Duk Labarai
Iyalan Mafarautan Da Aka Kashe A Edo Sun Yi Zanga-zangar Neman Diyya. Iyalan wasu mafarauta da suka rasa rayukansu a harin da ya faru a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga domin neman a biya su diyyar ‘yan uwansu da kuma gurfanar da wadanda suka aikata wannan mummunan laifi. Zanga-zangar, wadda ta gudana kwanaki 40 bayan aukuwar lamarin, ta samu halartar daruruwan ‘yan uwa da abokan arziki na wadanda abin ya shafa, wadanda suka fito dauke da takardu da hotunan wadanda suka mutu suna rokon gwamnati da hukumomin tsaro su dauki matakin gaggawa. Wani daga cikin shugabannin iyalan, ya bayyana cewa:"Har yanzu ba a kama ko daya daga cikin wadanda suka aikata wannan kisa ba. Mun gaji da jiran shiru. Muna so a tabbatar mana da adalci kuma a tallafa mana da diyya domin wadanda suka bar...
Ministan ilimi a Najeriya, Tunji Alausa ya ce hana satar amsa ne ya janyo faɗuwar ɗalibai a jarawabar shiga manyan makarantu da JAMB ke shiryawa a kowace shekara

Ministan ilimi a Najeriya, Tunji Alausa ya ce hana satar amsa ne ya janyo faɗuwar ɗalibai a jarawabar shiga manyan makarantu da JAMB ke shiryawa a kowace shekara

Duk Labarai
Ministan ilimi a Najeriya, Tunji Alausa ya ce hana satar amsa ne ya janyo faɗuwar ɗalibai a jarawabar shiga manyan makarantu da JAMB ke shiryawa a kowace shekara. Ya ce sakamakon zaɓen bana da aka samu, ya nuna irin yadda aka ƙara inganta yanayin rubuta jarabawar yadda ya kamata. Tunji ya bayyana haka ne yayin tattaunawa da gidan talabijin na Channels a Najeriya ranar Talata, inda ya ce hakan kuma ya nuna yadda tsarin rubuta jarabawar ya daƙile satar amsa da ɗalibai ke yi. Alausa ya ƙara da cewa kada a ɗauki akamakon zaɓen na JAMB a matsayin koma-baya, maimakon haka a kalle shi a matsayin yadda ɗaliban da suka ci suka nuna hazaƙa lokacin rubuta jarabawar. "JAMB na gudanar da jarabwarta ta hanyar amfani da tsarin kwamfuta wato CBT. Sun ɗauki ƙwararan matakai da ya janyo aka ...
Majalisar Dattawan Najeriya ta kafa kwamitin kula da mulkin jihar Ribas

Majalisar Dattawan Najeriya ta kafa kwamitin kula da mulkin jihar Ribas

Duk Labarai
Majalisar Dattawan Najeriya ta kafa kwamiti mai mambobi 18 domin sanya idanu kan yadda gwamnan riƙo na jihar Ribas Vice Admiral Ibok Ete Ibas mai ritaya ke tafi da aikinsa. Majalisar ta ce ta ɗauki matakin ne a wani yuƙuri na ƙarfafa shugabanci na gari ba tare da rufa-rufa ba a jihar da ke kudu maso kudancin Najeriya. Shugaban Majalsiar Dattawa Godswill Akpabio ya sanar yayin zaman majalisar na yau Talata cewa kafa kwamitin na da matuƙar mahimmancin wajen sa ido kan abubuwan da ke faruwa a jihar. Shugaban masu rinjaye Opeyemi Bamidele ne shugaban kwamatin, mambobin kuma sun haɗa da Adamu Aliero, da Osita Izunaso, da Osita Ngwu, da Kaka Shehu, da Aminu Abass, da Tokunbo Abiru, Adeniyi Adebire. A watan Maris ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci a Ribas sakamakon a...
‘Yànbìndìgà sun dame mu a Shanono da Bagwai, in ji ɗanmajalisar Kano

‘Yànbìndìgà sun dame mu a Shanono da Bagwai, in ji ɗanmajalisar Kano

Duk Labarai
Danmajalisar da wakiltar mazaɓar Ɓagwai da Shanono a Majalsar Wakilan Najeriya ya nemi ƙarin jami'an tsaro sakamakon abin da ya kira hare-haren 'yanfashin daji a yankin. Yusuf Badau ya yi kiran ne yayin wani ƙudiri da ya gabatar a gaban zauren majalisar yau Talata, inda ya lissafa lokutan da aka kai musu wasu hare-haren. "Yan bindigar sun fara kai hari ne wata kasuwa da ke garin Farin Ruwa a ƙaramar hukumar Shanono ranar 17 ga watan Afrilu, inda suka kashe mutum biyu, da raunata mutum shida kuma suka sace mutum ɗaya," in ji shi. "Sun sake kai irin wannan hari a garin Shanono ranar 26 ga watan Afrilun, sai dai mutanen garin sun tari ƴanbindigar kuma suka kore su. "A ranar 2 ga watan Mayu a garin Fafarawa da Sandamu na Shanono da Bagwai, sun yi garkuwa da mutum daya da sace wayoy...
An fitar da jadawalin kasashen Duniya 40 da suka fi farin ciki amma babu Najeriya a ciki

An fitar da jadawalin kasashen Duniya 40 da suka fi farin ciki amma babu Najeriya a ciki

Duk Labarai
Jadawalin kasashen Duniya da mutanensu suka fi farun ciki guda 40 kenan wanda kafar kungiyar World Happiness Report suka wallafa, saidai babu Najeriya a ciki. World's happiest countries. Finland Denmark Iceland Sweden Netherlands Costa Rica Norway Israel Luxembourg Mexico Australia New Zealand Switzerland Belgium Ireland Lithuania Austria Canada Slovenia Czechia UAE Germany United Kingdom United States Belize Poland Taiwan Uruguay Kosovo Kuwait Serbia Saudi Arabia France Singapore Romania Brazil El Salvador Spain Estonia Italy (World Happiness Report)
Da yiyuwar Tinubu ba zai iya tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 ba idan Amurka ta saki bayanai kan safarar miyagun kwayoyi da tace yayi-Inji Chief Eze Chukuemeka

Da yiyuwar Tinubu ba zai iya tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 ba idan Amurka ta saki bayanai kan safarar miyagun kwayoyi da tace yayi-Inji Chief Eze Chukuemeka

Duk Labarai
Da yiyuwar Tinubu ba zai iya tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2027 ba idan Amurka ta saki bayanai kan safarar miyagun kwayoyi da tace yayi. Ana zargin dai Shugaban kasa Tinubu da wasu mutane 3 a shekarun 90s sun yi safarar kwayoyi a birnin Chicago na Jihar Illinois ta kasar Amurka. An yi shari'a dan yanke musu hukunci amma ba'a san inda aka kwana ba Lauyoyi da ma sauran masu fafutuka na ta neman hukumar FBI da DEA su saki bayanai kan lamarin amma sai jan kafa suke inda lamarin ya dauki shekaru. Wasu dai na zargin akwai wata kullalliya a kasa game da kin fitar da bayanan.