Sunday, December 21
Shadow

Duk Labarai

Yajin aikin ma’aikatan NIMET ya hana wasu jirage tashi a Najeriya

Yajin aikin ma’aikatan NIMET ya hana wasu jirage tashi a Najeriya

Duk Labarai
Harkokin sufurin jiragen sama na fuskantar cikas a filayen tashi da saukar jiragen sama na cikin gida yayin da ma'aikatan hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ke gudanar da yajin aikin kan rashin ingancin yanayin aiki. Yajin aikin da ya yi kwana biyu yana gudana ya haifar da maƙalewar fasinjoji a filin jirgin saman Nnamdi Azikwe da ke Abuja, da filin jirgin Murtala Muhammed da ke Legas da sauran filayen jiragen sama da ke faɗin ƙasar. Kamfanin sufurin jiragen sama mafi girma a Najeriya, Air Peace ya sanar da dakatar da ayyukansa sakamakon yajin aikin. Kamfanin ya sanar da cewa ya yanke shawarar dakatar da sufurin jiragensa ne saboda kiyaye rayukan fasinjojinsa. Kafar yaɗa labarai ta Channels ta rawaito cewa a filin jirgin saman Legas, kamfanin XEJET da Aero Contractors, d...
Tsadar Rayuwa: Yanzu Tukunyar Shinkafa dafa duka Sai an kashe mata Naira 25,000 ake samun yanda ake so>>Inji SBM

Tsadar Rayuwa: Yanzu Tukunyar Shinkafa dafa duka Sai an kashe mata Naira 25,000 ake samun yanda ake so>>Inji SBM

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, a yanzu tukunyar shinkafa dafa duka wadda mutane 5 zasu iya ci a gida sai an kashe mata Naira 25,486 kamin ta bada abinda ake so. Hakan ya nuna an samu karin kaso 20 cikin 100 na farashin dafa shinkafar idan aka kwatanta da farashin dafata a watan Sarumba na shekarar 2024 wanda a wancan lokacin Naira 21,300 ake kashewa wajan Dafa shinkafar. SBM na fitar da bayanai akai-akai kan farashin dahuwar shinkafa kasancewarta itace abu mafi saukin sarrafawa a gidajen 'yan Najeriya. Kuma wannan farashi da suka bayyana suna maganar shinkafa ce wadda ta ji komai tun daga nama mai Albasa da komai dai da ake hadawa shinkafa dafa duka irin su kayan miya magi da sauransu. Sun alakanta hauhawar farashin da tashin farashin kayan masarufi wanda hauhawar farashin man fe...
Saurari Sabuwar Wakar Hamisu Breaker da Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta hana Saurare saboda Haramun ce tana karfafa Zìnà

Saurari Sabuwar Wakar Hamisu Breaker da Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta hana Saurare saboda Haramun ce tana karfafa Zìnà

Duk Labarai
Sabuwar Wakar Hamisu Breaker Ta Amanata ta gamu da fushin hukumar Hisbah a jihar Kano i da aka Haramta Saurarenta a jihar savoda tana karfafa Zìnà. Bayan da hutudole yawa wakar sauraren tsanaki da kuma bincike kan lamarin, mun gano cewa a wakar Hamisu ta Amanata ba mace, duka muryarsa ce. https://www.tiktok.com/@prince_abdool/video/7493982702161448197?_t=ZM-8vncFNyuyXt&_r=1 Inda matsalar take itace yanda mata ke kwaikwayon abinda ya fada daidai inda yake fara cewa "Mai Kishina ina sonki...." har zuwa karshe suna dorawa a kafafen sada zumunta. Misali kamar wannan ta kasa: https://www.tiktok.com/@khairatupcomingbackup/video/7495827859122982149?_t=ZM-8vnbxrfEPn3&_r=1 Wakar dai ba ta wani yi suna sosai ba, amma idan ba sa'a ba, wannan dakatarwar da Hisbah ta wa wa...
Hukumar Hizbah Ta Jihar Kano Ta Haramta Sauraron Wakar Hamisu Breaker Mai Suna ‘Amanata’ inda tace Zìnà wayar ke nunawa dan haka Haramunne sauraronta

Hukumar Hizbah Ta Jihar Kano Ta Haramta Sauraron Wakar Hamisu Breaker Mai Suna ‘Amanata’ inda tace Zìnà wayar ke nunawa dan haka Haramunne sauraronta

Duk Labarai
Hukumar Hizbah Ta Jihar Kano Ta Haramta Sauraron Wakar Hamisu Breaker Mai Suna 'Amanata' Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta yi kira ga matasa da su ƙauracewa sauraron waƙar Amanata ta Hamisu Breaker, tana mai cewar wannan waƙar haramun ce baki ɗaya. Mataimakiyar Babban Kwamandan Hisbah a ɓangaren Mata Dakta Khadija Sagir Sulaiman ce ta bayyana hakan, ta ce, waƙar ta fito ƙarara tana nuna źìña daga yadda mata suke hawa suna irin wani lanƙwashe-lanƙwashe da karya murya.
Wata Sabuwa: A yayin da suke shirin kulla alaka me karfi dan kwace mulki a 2027, an gano cewa Gwamnonin PDP sun daina daukar wayoyin Atiku da El-Rufai idan sun kirasu

Wata Sabuwa: A yayin da suke shirin kulla alaka me karfi dan kwace mulki a 2027, an gano cewa Gwamnonin PDP sun daina daukar wayoyin Atiku da El-Rufai idan sun kirasu

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa a yayin da tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ke shirin kulla alaka me karfi dan kayar da Tinubu a zaben shekarar 2027, Gwamnonin PDP sun daina daga wayarsu idan sun kirasu. Wani Jigo a jam'iyyar APC, Ayekooto Akindele ne ya bayyana hakan. Yace Gwamnonin PDP irinsu Ademola Adeleke basa daukar wayar Atiku da El-Rufai da rana a yanzu. Yana martanine kan rahoton dake cewa, Gwamnonin PDP din sun hada kai da Tinubu dan bashi goyon baya ya zarce a shekarar 2027. Ya kara da cewa, Babu yadda Atiku da El-Rufai zasu iya hana Tinubu zama shugaban kasa a shekarar 2027.
Wata Budurwa ta kàshè kanta saboda damuwar rayuwa a Abuja

Wata Budurwa ta kàshè kanta saboda damuwar rayuwa a Abuja

Duk Labarai
Rahotanni daga babban birnin tarayya, Abuja na cewa, wata budurwa ta kashe kanta. Lamarin ya farune a rukunin gidaje na CITEC dake Life Camp, babban Birnin Tarayya, Abuja ranar April 22, 2025. An iske matar da misalin karfe 7:00 a.m. rataye a jikin wata kwantena inda 'yansanda suka isa wajen suka tafi da ita zuwa FMC Jabi inda a canne likitoci suka tabbatar da ta mutu. An dai gano wayarta sannan an fara bincike kan lamarin.
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 

2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 

Duk Labarai
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara. Tsohon mashawarcin shugaban kasa, Dr. Hakeem Baba-Ahmed, ya bukaci shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, da ya hakura da shirin neman tazarce, ya bai wa matasa dama su yi takara domin ciyar da kasa gaba a babban zabe na 2027. A wata budaddiyar wasika da ya aike wa Daily Trust a ranar Laraba, Baba-Ahmed ya roki Tinubu da ya yi watsi da duk wani shirin sake tsayawa takara a 2027. Baba-Ahmed ya bayar da hujjar cewa, Tinubu ya ajiye son ransa, ya bar matasa a mulki, ya fice daga Siyasa a mutunce, shi ne dattaku da barin baya da kyau. “Ka koma gefe – ba wai kabar wa abokan hamayyarka takara ba, amma don sabbin jini matasa ‘yan Nijeriya da za su iya ciyar da al’umma gaba da sabbin kuzari da tunani.” in ji shi. ...
Shawarar da kuke baiwa shuwagabannin mu na jefa mutane cikin talauci da Yunwa>>NLC ta gayawa IMF

Shawarar da kuke baiwa shuwagabannin mu na jefa mutane cikin talauci da Yunwa>>NLC ta gayawa IMF

Duk Labarai
Kungiyar Kwadago ta kasa, NLC ta gayawa kungiyar bada Lamuni ta Duniya IMF cewa shawarwarin gyara da suke baiwa shuwagabannin Najeriya na jefa mutane cikin halin kaka nikayi. NLC ta gayawa IMF hakane a yayin da wakilan IMF din suka zo Najeriya suka je ofishin NLC dan su ji yanda ake ciki game da irin abinda 'yan Najeriya ke cewa kan tsare-tsaren gwamnati. Wakilan IMF biyu, Christian H. Ebeke da Axel Schimmelpfennig ne suka wakilci kungiyar zuwa ofishin NLC. Sun bayyana cewa, IMF tana bayar da shawara ne kawai, bata tursasa kasashe amfani da shawarwarin da take basu. Sannan sun ce mafi yawanci kasashe basa aiwatar da shawarwarin IMF din yanda ya kamata. A nasa bangaren shugaban NLC Joe Ajaero ya bayyana cewa tsare-tsare irin su cire tallafin mai wanda dama can babu shi kawai ...