Monday, December 15
Shadow

Duk Labarai

Farashin ɗanyen man fetur ya yi mummunar faɗuwa a kasuwar duniya wadda rabon da aka irinta tun shekaru 5 da suka gabata, kudin shigar Najeriya zasu samu Gibi

Farashin ɗanyen man fetur ya yi mummunar faɗuwa a kasuwar duniya wadda rabon da aka irinta tun shekaru 5 da suka gabata, kudin shigar Najeriya zasu samu Gibi

Duk Labarai
Farashin ɗanyen man fetur samfurin Brent - wanda aka fi yawan ƙayyade farashi da shi a duniya - ya yi faɗuwa mafi muni cikin shekara biyar. Faɗuwar da kusan kashi 3.2 cikin 100 - zuwa dala 63.49 kowace ganga - ta faru ne a yau Litinin da misalin ƙarfe 11:00 agogon Najeriya da Nijar. Rabon ya yi irin faɗuwar tun watan Afrilun 2021. Shi ma samfurin West Texas Intermediate (WTI) ya faɗi zuwa kashi 3.58, kamar yadda kamfanin labarain na Reuters ya ruwaito. Faɗuwar farashin ta faru ne sakamakon sanarwar da Shugaban Amurka Donald Trump ya bayar ta ƙaƙaba wa dukkan ƙasashen duniya ƙarin harajin shifgar da kaya ƙasarsa. Hakan ya sa samfurin Brent ya faɗi da kashi 10.9 cikin 100, yayin da shi ma WTI ya faɗi da 10.8.
Saudiyya ta ayyana ranar da masu aikin Umrah za su fice daga kasar

Saudiyya ta ayyana ranar da masu aikin Umrah za su fice daga kasar

Duk Labarai
Ma'aikatar aikin Hajj da Umrah ta Saudi Arabiya ta kebe ranar 1 ga watan Dhul Qada, wadda ta zo dai-dai da 29 ga watan Afrilu, a matsayin ranar karshe da duk wani bako da ya shiga kasar domin yin Umrah ya fice. Ma'aikatar ta ce ta dauki matakin ne domin fara gudanar da shirye-shiryen aikin Hajji mai zuwa. Cikin wata sanarwa, ma'aikatar ta ce ranar 15 ga watan Shawwal, da ya yi dai-dai da 13 ga watan Afrilu, ita ce ranar karshe da masu shiga kasar domin aikin Umrah za su daina shiga, sai dai a fita. Ma'aikatar ta jaddada cewa duk wanda aka samu ya ci gaba da zama a kasar har ya wuce lokacin da kebe, to ko shakka babu ya saba ka'ida sannan kuma zai fuskanci hukunci. Daga nan ta bukaci mutane da ma kamfanonin da ke shirya zuwa aikin Umrah da su kiyaye da wadannan lokuta da aka kay...
Gwamnonin APC sun kai wa Muhammadu Buhari ziyara

Gwamnonin APC sun kai wa Muhammadu Buhari ziyara

Duk Labarai
Kungiyar gwamnonin jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya karkashin jagorancin shugabanta gwamnan Imo Sanata Hope Uzodinma, ta kai wa tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ziyarar ban girma a gidansa da ke Kaduna. Bayan shugaban kungiyar, sauran gwamnonin da suke cikin tawagar ma su ziyarar sun hada da gwamnan Kaduna da na Gombe da Kwara da Nasarawa da Ebonyi da Kebbi da Edo da Kogi da Ondo da Ekiti da kuma Benue. Sauran 'yan tawagar sun hadar da mataimakin gwamnan Jigawa da ministan kasafin kudi da tsare-tsare.
Najeriya da Saudiyya sun ƙulla yarjejeniyar yaƙi da miyagun ƙwàyòyì

Najeriya da Saudiyya sun ƙulla yarjejeniyar yaƙi da miyagun ƙwàyòyì

Duk Labarai
Najeriya da Saudi Arabiyya sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimta domin karfafa yaki da hada-hadar kwayoyi. A ranar Litinin Hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta NDLEA ta Najeriya da kuma Hukumar da ke yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta Saudiyya GDNC, suka sanya hannu kan yarjejeniyar a Riyadh. Cikin wata sanarwar da daraktan yada labarai na hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi, ya fitar ya ce kasashen biyu sun amince su kara karfafa yaki da fataucin miyagun kwayoyi a dukkan iyakokinsu. Da ya ke magana a wajen sanya hannu kan yarjejeniyar, shugaban hukumar ta NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa, mai ritaya, ya ce dukkan kasashen sun jima suna yin hadaka da bangarori daban daban. Marwa, wanda ya samu rakiyar darakta a sashen bincike da gudanarwa na hukumar, Ahmed Ning...
Mun san ana cutar mu, ba sai wani dan iska Munafiki Dan Bello ya fito ya gaya mana ba>>Inji Sheikh Adam Muhammad Albaniy Gombe

Mun san ana cutar mu, ba sai wani dan iska Munafiki Dan Bello ya fito ya gaya mana ba>>Inji Sheikh Adam Muhammad Albaniy Gombe

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Babban malamin Addinin Islama, Sheik Adam Muhammad Albany Gombe ya soki Dan Bello kan labarin zargin daya wallafa na cewa, an baiwa shugaban kungiyar Izala, Sheik Bala Lau kudin gina Azuzuwan makarantu daga Gwamnatin tarayya amma bai gina ba. Malam ya bayyana Dan Bello a matsayin wanda yake can kasar waje yake gayawa mutane cewa wai ana cutarsu inda yace 'yan Najeriya sun san ana cutarsu ba sai wani Dan Bello ya fito yana gaya musu ba. Hakanan ya gargadi Dan Bello da cewa zasu ma...
Nijar ta ayyana Hausa a matsayin harshen da za’a rika amfani dashi a ƙasar

Nijar ta ayyana Hausa a matsayin harshen da za’a rika amfani dashi a ƙasar

Duk Labarai
A Jamhuriyar Nijar gwamnatin kasar ta bayyana Hausa a matsayin harshen da za a rinka amfani da shi a kasar yayin da sauran harsuna ta ayyanasu a matsayin na magana. Kazalika an kuma bayyana harshen Ingilishi da Faransanci a matsayin harsunan aiki. To sai dai kuma ba dukkanin 'yan kasar ne ke maraba da wannan mataki ba. An kiyasta cewa akwai mutum miliyan 18 da ke jin harshen hausa a Jamhuriyar Nijar, abin da ake ganin wannan ne ya sanya gwamnatin kasar ta ayyana shi a matsayin harshen da za a rinka amfani da shi a kasar. To sai dai kuma ba dukkanin 'yan kasar ne wannan mataki ya yi wa dadi ba, inda wasu ke cewa ya kamata a yi nazari sosai a kai. Harshen Hausa shi ne ke matsayin na uku a Afirka inda kasashe da dama a Afirka a ke samun masu jin harshen. Akwai dai masu jin h...
Trump ya yi barazanar kara wa China harajin kashi 100

Trump ya yi barazanar kara wa China harajin kashi 100

Duk Labarai
Shugaba Donald Trump, na Amurka, ya yi barazanar zafafa yaƙin kasuwanci da ke tsakaninsu da China, ta hanyar kakaba karin harajin kashi 50 cikin 100 na kayayyakinsu, muddin Beijing ba ta jingine shirinta na mayar da martani ba. A wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump, ya ce zai kawo karshen duk wata yarjejeniya da ke tsakaninsu, muddin China ba ta yi biyayya ba. Wannan harajin da Trump ke shirin sanya wa China zai haura kashi 100 cikin 100. A mako mai zuwa ne haraje-harajen da China ta sanya ita ma kan kayayyakin Amurka za su soma aiki.
Tun farko gayyatar da shelkwatar ƴansanda ta yi wa Sarki Sanusi ba ta da amfani – Peter Obi

Tun farko gayyatar da shelkwatar ƴansanda ta yi wa Sarki Sanusi ba ta da amfani – Peter Obi

Duk Labarai
Peter Obi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP), ya yaba wa Rundunar ‘Yansandan Najeriya bisa janye gayyatar da ta aikewa Muhammadu Sanusi, Sarkin Kano. A makon da ya gabata ne, ‘yansanda suka gayyaci Sanusi zuwa hedikwatar rundunar domin yi masa tambayoyi kan zargin kashe-kashe da suka faru a lokacin bikin Eid-el-Fitr da ya gabata. Da yake mayar da martani a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin, Obi ya ce hanyar warware matsalar a matakin ƙasa-ƙasa (wato ba tare da tursasawa daga sama ba) zai ƙara kawo zaman lafiya da amincewar jama’a. Tsohon gwamnan jihar Anambra ya ce ba bu buƙatar wannan gayyata tun da farko, kuma hakan na iya tayar da hankali a lamarin da tuni ya ɗauki zafi. “Ina so in yaba wa Rundunar ‘Yansandan Najeriya sab...
Hotuna: Wani mai tallar Goro ya shiga damuwa jim kaɗan bayan ya gama liƙawa Alan Waka kudin cinikinsa a bikin Sallar aka aka gabatar a fadar sarkin Kano dake Nasarawa

Hotuna: Wani mai tallar Goro ya shiga damuwa jim kaɗan bayan ya gama liƙawa Alan Waka kudin cinikinsa a bikin Sallar aka aka gabatar a fadar sarkin Kano dake Nasarawa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wani mai tallar Goro ya shiga damuwa jim kaɗan bayan ya gama liƙawa Alan Waka kudin cinikinsa a bikin Sallar aka aka gabatar a fadar sarkin Kano dake Nasarawa Menene ra'ayoyin ku?
‘Yansanda sun Tarwatsa masu zanga-zangar adawa da tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da ‘yan Jarida suka banka musu barkonon tsohuwa a jihar Rivers da Abuja

‘Yansanda sun Tarwatsa masu zanga-zangar adawa da tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da ‘yan Jarida suka banka musu barkonon tsohuwa a jihar Rivers da Abuja

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa 'yansanda a Jihar Rivers sun tarwatsa masu zanga-zangar adawa da tsare-tsaren gwamnatin Tinubu da suka fito a yau, Litinin. Rahoton yace da misalin karfe 9 na safe ne matasan masu zanga-zangar suka fito inda suka ci karo da dandazon 'yansanda a filin Isaac Boro Park dake birnin na Fatakwal. 'Yansandan aun gayawa matasan cewa ba zasu barsu su yi zanga-zangar ba amma matasan sun ce sai sun yi. 'Yansandan sun harbawa matasan barkonon tsohuwa sannan suka bisu da duka ciki hadda 'yan jarida da suka je daukar lamarin. Hakanan a babban birnin tarayya, Abuja ma, 'yansandan sun bankawa matasa masu zanga-zangar barkonon tsohuwa da suka fito yin zanga-zangar a maitama. Wannan rana ta Zanga-zangar dai ta zo daidai da ranar 'yansanda ta Najeriya. Dan haka n...