Tuesday, February 17
Shadow

Duk Labarai

An naushi wani ya mùtù yayin da ya je rabon fada a jihar Adamawa

An naushi wani ya mùtù yayin da ya je rabon fada a jihar Adamawa

Duk Labarai
Wani mutum da ya je rabon fada a jihar Adamawa an nausheshi ya mutu. Mutumin me suna Markus Dali ya shiga tsakanin Barka Yama da Alex Tari dake fada suna naushin juna da niyyar ya rabasu. A nan ne Barka Yarma ya nausheshi wanda shine yayi sanadiyyar mutuwarsa. Lamarin ya farune a kauyen Sina Kwande dake karamar hukumar Michika ta jihar Adamawan. Tuni dai aka kama Barka aka kuma gurfanar dashi a gaban kotun Magistrate dake Yola. Wanda ake zargi dai ya amsa laifinsa inda aka kaishi gidan yari. Kotun ta mika maganar wajan hukumar bayar da shawara kan irin lamurran dan sanin hukuncin da ya dace dashi.
A cikin mu,Sanatoci akwai ‘yan kwàyà da masu taimakawa masu safarar kwàyà, idan kuma kun yi gaddama, muje kowa a mai gwajin kwàyà ko kuma mu rantse da Qur’ani bama harkar kwàyà>>Sanata Kawu Sumaila ya kalubalanci Abokan aikinsa Sanatoci

A cikin mu,Sanatoci akwai ‘yan kwàyà da masu taimakawa masu safarar kwàyà, idan kuma kun yi gaddama, muje kowa a mai gwajin kwàyà ko kuma mu rantse da Qur’ani bama harkar kwàyà>>Sanata Kawu Sumaila ya kalubalanci Abokan aikinsa Sanatoci

Duk Labarai
A yayin da majalisar Dattijai ke tattauna batun kirkirar kudirin dokar da zai samar da ma'aikatar wayar da kai akan ta'ammuli da miyagun kwayoyi da dawo da wanda suke cikin harkar kan tafarkin daidai, Sanata Kawu Sumaila ya zargi Sanatoci da hannu a harkar. https://www.youtube.com/watch?v=Erpx2vDE5yE?si=ZdJl7UOfms9FTTcj Sanata Sumaila ya bayyana cewa, akwai sanatoci da yawa dake da alaka da masu safarar kwaya da kuma wanda ma suna shanta. Yace akwai wanda suke da tulin miyagun kwayoyin a gidajensu da mazabunsu, sannan akwai da yawa wadanda suke amfani da miyagun kwayoyin lokacin zabe su baiwa matasa dan cimma burikansu na siyasa. Yace dan haka ta kansu ya kamata a fara wannan gyara. Yace idan sun yi gaddama dukansu su je a musu gwayin shan miyagun kwayoyi sannan kuma kowa ...
Duk da akwai wahala amma sai Gwamnati ta ci gaba da tsarin da take kai a yanzu na tsawon shekaru 15 kamin Najeriya ta ci gaba>>Bankin Duniya

Duk da akwai wahala amma sai Gwamnati ta ci gaba da tsarin da take kai a yanzu na tsawon shekaru 15 kamin Najeriya ta ci gaba>>Bankin Duniya

Duk Labarai
Bankin Duniya ya baiwa Gwamnatin Najeriya shawarar cewa ta ci gaba da tsarin da take kai a yanzu na tsawon shekaru 10 ko 15 idan tana son samun ci gaba ba a Afrika kadai ba harma da Duniya baki daya. Wakilin bankin Duniyar, Indermit Gill ne ya bayyana haka a wajan wani taron tattalin arziki da ya gudana a Abuja. Ya kawo tsare-tsaren gwamnati na cire tallafin dala da mai da saransu wanda ya ce ya kamata a ci gaba da aikatasu dan samun ci gaba me dorewa. Saidai a yayin da yake jawabin, an rika masa ehon ba'a son wannan shawara tasu ta bankin Duniya amma du da haka yace ba lallai ne a yadda da abinda yake fada ba amma gaskiyace.
Gwamnatin Tarayya zata sakawa masu samun kudi da yawa sabon Haraji

Gwamnatin Tarayya zata sakawa masu samun kudi da yawa sabon Haraji

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya zata sakawa masu samun kudi fiye da Naira Miliyan 100 sabon haraji na kaso 25 cikin 100. Shugaban kwamitin shugaban kasa dake kula da haraji da tsare-tsaren kudade, Taiwo Oyedele ne ya bayyana haka inda yace gwamnati zata fara sakawa maau kudi sosai haraji me yawa. Yace sabon harajin zai fara aiki ne nana da shekarar 2025. Yace mafi yawancin 'yan Najeriya basa biyan haraji saboda rashin yadda da gwamnati. Yace yanzu haka kudirin dokar karin harajin yana gaban majalisar tarayya. Yace zasu samar da yanayin da za'a rika samun bayanai kan biyan Harajin a bayyane kamar yanda kasar Afrika ta kudu ta yi. Ya kuma koka da cewa kaso 17 cikin 100 na 'yan Najeriya ne kadai ke biyan haraji.
‘Yan kwallon Najeriya sun yi fushi sun dawo gida Najeriya ba tare da buga wasa da kasar Libya ba bayan da kasar ta Libya ta wulakantasu ta barsu a filin jirgi

‘Yan kwallon Najeriya sun yi fushi sun dawo gida Najeriya ba tare da buga wasa da kasar Libya ba bayan da kasar ta Libya ta wulakantasu ta barsu a filin jirgi

Duk Labarai
'Yan kwallon Kafa na Najeriya Super Eagle sun yi fushi sun dawo gida Najeriya bayan da kasar Libya ta wulakantasu. A baya dai mun kawo muku yanda kasar Libya ta karkatar da jirgin saman Najeriya da gangan zuwa wani gari na daban dake da tazarar tafiyar awanni 2 tsakaninsa da inda zasu buga wasa da kungiyar kwallon kafar ta Libya. Hakan yasa 'yan wasan Najeriyar suka kwashe awanni 13 a filin wasan ba tare da kulawa ba. A karshe dai bisa umarnin hukumar kwallon kafa ta Najeriya, 'Yan kwallon Na Najeriya sun dawo gida ba tare da buga wasa da kasar ta Libya ba. Dama dai wasan na samun gurbin buga gasar cin kofin Nahiyar Africa shine zai tabbatar da zuwan Najeriya gasar da ta bugashi.
Hotuna: Kasar Libya ta kulle ‘yan kwallon Najeriya a filin jirgi ta hanasu zuwa ko ina

Hotuna: Kasar Libya ta kulle ‘yan kwallon Najeriya a filin jirgi ta hanasu zuwa ko ina

Duk Labarai
Kungiyar 'yan Kwallon Najeriya ta Super Eagle tana can a filin jirgin kasar Libya a tsare inda aka hanasu zuwa ko ina. 'Yan kwallon dai sun je kasar ta Libya ne dan buga wasa zagaye na biyu da kungiyar kwallon kafar kasar ta Libya bayan sun yi nasara da sakamakon 1-0 a zagayen farko da aka buga a Najeriya. Awanni kadan kamin saukar jirgin na 'yan Super Eagle a Libya sai aka canja masa wajan sauka zuwa wani birni me nisa tsakaninshi da inda za'a buga wasa. Bayan saukar 'yan kwallon Najeriyar sai ba'a basu motar da zata kaisu inda zasu buga wasan ba, sannan rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin Najeriya ta yi kokarin samarwa da 'yan wasan Najeriyar motar da zata kaisu filin wasan amma hukumomin kasar ta Libya suka hanasu fita daga filin wasan. Ana ganin wannan kamar ramuwa kas...
Dara Ta ci Gida: Bayan Gyaran da tawa Sanata Shehu Sani,Matar Tsohon Gwamnan Kaduna, Hadiza El-Rufai ta kuma yiwa danta, Dan majalisar tarayya,Hon. Bello El-Rufai gyaran Turanci shima

Dara Ta ci Gida: Bayan Gyaran da tawa Sanata Shehu Sani,Matar Tsohon Gwamnan Kaduna, Hadiza El-Rufai ta kuma yiwa danta, Dan majalisar tarayya,Hon. Bello El-Rufai gyaran Turanci shima

Siyasa
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} A dazu ne muka kawo muku labarin yanda dambarwa ta kaya tsakanin tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya, Sanata Shehu Sani da matar tsohon Gwamnan Kaduna,Hajiya Hadiza El-Rufai bayan da ta masa gyaran turanci. Sanata Shehu Sani dai bai ji dadin gyaran turancin da Hajiya Hadiza Eta masa ba inda yace dan Allah ta kyaleshi. Saidai da yake abin nata ba zabe bane tsakani da Allah take yi, a yanzu kuma Hajiya Hadiza El-Rufai gyaran nata ya kawo kan danta, wanda dan majalisar tarayya ne watau Hon. Bello El-Rufai...
Kalli Hotuna yanda dan bautar kasa ya rame bayan shekara daya saboda wahalar Gwamnatin Tinubu

Kalli Hotuna yanda dan bautar kasa ya rame bayan shekara daya saboda wahalar Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wannan wani dan bautar kasa ne da ya bayyana cewa wahalar gwamnatin Tinubu tasa ya rame a cikin shekara daya. https://twitter.com/Sadeeq_Malo/status/1845000308331594194?t=Jmv5p_8avlv0IhnVwObctA&s=19 Hotunan nashi sun dauki hankula a shafukan sada zumunta inda akaita bayyana ra'ayi da mamakin yanda ya canja.
Duk inda kuka ga banza ta fadi, zaku ci abinci kyauta, kada ku yi wasa da wannan damar ku ci>>Kakakin Majalisar Dattijai, Godswill Kapadia ya baiwa ‘yan Najeriya shawara

Duk inda kuka ga banza ta fadi, zaku ci abinci kyauta, kada ku yi wasa da wannan damar ku ci>>Kakakin Majalisar Dattijai, Godswill Kapadia ya baiwa ‘yan Najeriya shawara

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kakakin majalisar Wakilai, Godswill Akpabio ya baiwa 'yan Najeriya shawarar cewa duk inda suka ga banza ta fadi ta cin abinci kyauta, kada su yi wasa da wannan damar. Bidiyon bayanin nasa ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda ake ta bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai. https://www.youtube.com/watch?v=fIdtxSZDQoY A baya dai Akpabio ya baiwa 'yan Najeriya shawarar su rage yawan motocin da suke hawa saboda tsadar man fetur.
Kada wanda ya kara kiran shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da su an banza na T-Pain>>Fadar shugaban kasa ta yi gargadi

Kada wanda ya kara kiran shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da su an banza na T-Pain>>Fadar shugaban kasa ta yi gargadi

labaran tinubu ayau
Fadar shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ta yi gargadin kada wanda ya kara kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sunan banza na T-Pain. Sunan T-Pain dai a kafar sada zumunta aka sakawa shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu shi dan nuna wahalar da mutane ke ciki a karkashin Gwamnatinsa wanda sunan wani mawakin kasar Amurka ne. Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar na daga cikin wadanda suka rika kiran Tinubu da wannan suna. Saidai duk da gargadin da fadar shugaban kasar ta yi,da yawa sun ce ba zasu daina fadar wannan suna ba.