Saturday, January 3
Shadow

Duk Labarai

Hoto: ‘Yan Sanda Sun Cafke Masu Karbar Adai-daita Sahu Na Sata

Hoto: ‘Yan Sanda Sun Cafke Masu Karbar Adai-daita Sahu Na Sata

Tsaro
Jami’an ‘yan sanda a jihar Adamawa sun kama wasu matasa biyu da ake zargi da karbar babur mai uku na sata. Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta bayyana hakan a wata sanarwa da ta samu ranar Alhamis, inda ta ce ta kuma kwato babur din da aka sace. “A ranar 28 ga watan Mayu, 2024, rundunar ‘yan sandan Adamawa ta samu bayanai game da wani keken napep da aka sace a kan titin Chochi, Rumde, Yola ta Arewa” in ji rundunar a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai daukar hotonta na SP Suleiman Nguroje. “Bayan samun labarin, an tura tawagar ‘yan sanda masu sanya ido a hedikwatar Jimeta Divisional ba tare da bata lokaci ba. An yi sa’a, an kama wani Yusuf Adamu mai shekara 18 da kuma Abdul Salam Abubakar mai shekaru 18 a lokacin da suke kokarin sayar da babur din,” in ji ‘yan sandan. ...
YANZU – YANZU: Shugaba Tinubu ya roƙi kungiyar dattawan Arewa su ja kunnen Gwamnonin yankin dake zuwa su tare a Abuja bayan sun ci zabe

YANZU – YANZU: Shugaba Tinubu ya roƙi kungiyar dattawan Arewa su ja kunnen Gwamnonin yankin dake zuwa su tare a Abuja bayan sun ci zabe

Siyasa
YANZU - YANZU: Shugaba Tinubu ya roƙi kungiyar dattawan Arewa su ja kunnen Gwamnonin yankin dake zuwa su tare a Abuja bayan sun ci zabe. Majiyar mu ta a yau ta ruwaito Shugaban ya ce yana bakin ƙoƙarinsa a matakin tarayya amma ya kamata a sanya ido kan Gwamnoni su ma su riƙa yin abunda ya dace, su taimaki talakawa, "A lokacin zaɓe ana bin mutane lungu-lungu, gida-gida don neman ƙuri'unsu amma da zaran anci zabe sai kaga Gwamna ko dan siyasa ya tare a Abuja ya mance da talakawansa" inji Tinubu. Me zaku ce?
Hotuna:Kalli ta’addancin da ‘yan Kungiyar I-POB dake son kafa kasar Biafra suka yi na kona motoci da kashe mutane a jiya Laraba

Hotuna:Kalli ta’addancin da ‘yan Kungiyar I-POB dake son kafa kasar Biafra suka yi na kona motoci da kashe mutane a jiya Laraba

Tsaro
Rahotanni sunce a jiya, Laraba, 'yan Bindigar da ake kira da wanda ba'a sani ba amma ake kyautata zaton 'yan kungiyar IPOB ne dake son kafa kasar Biafra sun kai hari kan kasuwar Nkwo Ibagwa dake karamar hukumar Igbo-Eze South ta jihar Enugu. 'Yan bindigar sun rika harbi a iska wanda yayi sanadiyyar kisan wannan matashin da hotonsa ke kasa. 'Yan uwa da abokan arziki da yawa sun koka da rashin wannan matashi da aka yi inda da yawa suka hau shafukan Facebook suke alhinin rashin matashin. Hakanan rahoton Sahara Reports yace 'yan Bindigar sun kona kayan 'yan kasuwa da motoci wanda aka yi kiyasin sun kai na miliyoyin Naira.
Gwamnatin tarayya ta gayyaci kungiyar kwadago, NLC ta dawo a ci gaba da tattaunawa game da mafi karancin Albashi

Gwamnatin tarayya ta gayyaci kungiyar kwadago, NLC ta dawo a ci gaba da tattaunawa game da mafi karancin Albashi

Siyasa
A jiya Laraba, wasu majiyoyi sun bayyana cewa, Gwamnatin tarayya ta gayyaci kungiyar Kwadago ta dawo a ci gaba da tattaunawa kan maganar mafi karancin Albashi. A zama na karshe dai an tashi baram-baram bayan da NLC din taki amincewa da Naira dubu 60 a matsayin mafi karancin Albashi. Hakanan wata majiyar tace kungiyar kwadagon ta amince da cewa zata amsa gayyatar ta gwamnati. Kungiyar dai ta baiwa Gwamnati nan da karshen watan Mayu da muke ciki a gama maganar mafi karancin Albashin ko kuma ta tafi yajin aiki.
Jirgin kasa dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja ya taka tare da kashe yara mata tagwaye a jihar Naija

Jirgin kasa dake jigila tsakanin Kaduna zuwa Abuja ya taka tare da kashe yara mata tagwaye a jihar Naija

Duk Labarai
Jirgin kasan daya taso daga Abuja zuwa Kaduna ya kashe kananan yaran wanda tagwayene mata a karamar hukumar Tafa. Lamarin ya farune da misalin karfe 10 na safe ranar Asabar, kamar yanda jaridar The Cable ta ruwaito. Yaran, Hassana and Hussaina Baro shekarar su daya da watanni 6. Kakakin 'yansandan jihar Naija, Wasiu Abiodun ya tabbatar da daruwar lamarin. Yace yaran suna wasa ne akan titin jirgin kasan kamin lamarin ya faru.
Hotuna:Sojojin kasar Nijar sun kama kasurgumin dan Bindigar nan, Kachalla Baleri

Hotuna:Sojojin kasar Nijar sun kama kasurgumin dan Bindigar nan, Kachalla Baleri

Tsaro
Sojojin kasar Nijar sun kama kasurgumin dan Bindiga, Kachalla Baleri. Masanin harkar tsaro, Zagazola Makama ne ya bayyana hakan inda yace an kamashine a Rouga Kowa Gwani. Baleri wanda dan Shinkafine ya addabi mutane a Zamfara, Sokoto da Maradi. Ya jagorancin kisan mutane da yawa da kuma garkuwa da mutane da yawa. Yana daya daga cikin na hannun damar Kachalla Bello Turji kuma shine mutum na 40 mafi hadari da sojojin Najeriya suke nema ruwa a jallo.
Hotuna: Matashi Ya Raba Litattafai Gudu Dubu Goma Kyauta Ga Dalibai Domin Taya Gwamna Abba Murna Cika Shekara Guda Akan Mulki

Hotuna: Matashi Ya Raba Litattafai Gudu Dubu Goma Kyauta Ga Dalibai Domin Taya Gwamna Abba Murna Cika Shekara Guda Akan Mulki

Duk Labarai
Matashi Ya Raba Litattafai Gudu Dubu Goma Kyauta Ga Dalibai Domin Taya Gwamna Abba Murna Cika Shekara Guda Akan Mulki Shugaban Gidauniyar Sharu Sarakin Kwankwasiyya free computer training, Hon. Sharu Saraki ya rabawa dalibai littafin kimanin dubu goma domin taya Mai girma Gwamnan Kano Eng. Abba Kabir Yusuf murnar cika shekara daya akan mulki. Sannan kuma gidauniyar ta sake daukar nauyin dalibai mata ilimin kwamfuta kyauta a gidaunyar dake kan titin Airport road kusa da gidan man Danmarna kwanar kotun No-Man's-land.