
Jami’an hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa, EFCC, sun kama ƴar bokon nan kuma ƴar kasuwa, Aisha Sulaiman Achimugu.
Lauyan Achimugu, Chikaosolu Ojukwu ne ya shaida wa Nairametrics a wani sako da ya aike a safiyar yau Talata.
Ya ce an kama Achimugu daga saukar ta daga jirgi bayan ta dawo daga London da misalin ƙarfe 5 na asuba.
Tun a baya, lauyan Achimugu ya baiyana wa babbar kotun tarayya a Abuja cewa a yau wacce ya ke karewa za ta kai kan ta ga EFCC a binciken zargin da ake mata na karkatar da wasu kuɗaɗe.