Wednesday, April 15
Shadow

Da Duminsa: A karshe dai ICPC ta saka ranar da zata Gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban kotun Gwamnatin tarayya

Hukumar yaki da rashawa ta ICPC ta bayyana cewa ta shirya tsaf dan gurfanar da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai a gaban babbar kotun tarayya dake Kaduna.

Hukumar tace za’a gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne bisa zargin Almundahanar kudade, damfara da kuma amfani da ofishinsa ta hanyar da bata dace ba.

Sanarwar tace za’a gurfanar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai ne tare da wani me suna  Joel Adoga ranar 24 ga watan Maris.

Hakanan sanarwar tace akwai shari’a ta daban itama da za’a shigar da tsohon gwamnan Kadunan a babbar kotun jihar kaduna itama inda ake zarginsa da aikata ba daidai ba da ofishinsa da kuma karkatar da kudade.

Karanta Wannan  Gaddama ta kaure tsakanin Sowore da EFCC inda ya zargesu da yin rufa-rufa akan maganar kwace gidaje 753

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *