Tuesday, February 10
Shadow

Da Duminsa: An samu Baraka a jam’iyyar APC, ji maganganu marasa dadi da Wike yake gayawa shugaban kasa

Wani Bidiyon Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya bayyana inda aka jishi yana wata barazana.

An ji Wike na barazanar ne a wajan wani taron siyasa a jiharsa.

Ya bayyana cewa mutum kada ya zo ya kawo musu abinda ba shi kenan ba a jihar Rivers.

Wike bai fadi da wanda yake ba inda yace mutum ya tambayi abinda ya faru da wadanda suka yi yunkurin yiwa jihar Rivers kutse a baya.

saidai wasu sun ce da sakataren Jam’iyyar APC yake inda wasu kuma ke cewa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yake.

Karanta Wannan  Gwamnoni na farin ciki da cire tallafin man fetur kuma in ku baku jin dadi, su suna jin dadin cire tallafin>>Inji Me magana da yawun shugaban kasa, Daniel Bwala

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *