Friday, July 17
Shadow

Da Duminsa: Kasar Amurka na shirin saka Kwankwaso cikin mutanen da zata hana Visa da shiga kasarta

Rahotanni sun bayyana cewa, kasar Amurka na shirin hana tsohon gwamnan Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso Visa ta shiga kasarta da kuma kwace kadarorin sa dake kasar.

Hakan na kunshene cikin wata kudirin doka da wasu ‘yan majalisun kasar su 5 suka gabatar inda suke neman a saka wa wasu ‘yan Najeriya dake dakile ‘yancin addini takunkumin shiga kasar Amurka.

Daga cikin wanda ake zargi ake kuma shirin kakabawa wannan takunkumi akwai kungiyar Miyetti Allah da sauransu.

Karanta Wannan  Sanata Natasha Akpoti zata gurfana a gaban kotu bisa karar da Gwamnatin Tarayya ta kaita na bata suna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *