
Tauraruwar fina-finan Hausa, Amal Umar ta bayyana cewa, ta daina siyasa.
Ta bayyana cewa tun a farkon mulkin Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta daina tallata Gwamnatinsa.
Tace dalili shine bata son ta tallatawa mutane wanda daga baya zai zo yayi ba daidai ba a zo a zageta, dan haka tace masu mata maganar siyasa a comment ma su daina.
Amal ta kara da cewa, ko nawa za’a bata ta hakura, Mutuncinta yafi mata komai.