Wednesday, May 13
Shadow

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikawa majalisa bukatar ciwo bashin Dala Miliyan $516

Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aikawa majalisar Dattijai da bukatar ciwo bashin dala Miliyan $516.

Shugaban ya aika da bukatar ne a yau, Alhamis inda yace za’a yi aikin gina titin Sokoto-Badagry ne da kudaden.

Kakakin majalisar, Godswill Akpabio ya bayyana cewa akwai bukatar a gaggauta amincewa da karbo bashin.

Ya bayyana cewa, ya baiwa kwamitin kula da bashi na majalisar umarnin su kammala amincewa da bashin cikin sati daya.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Gwamnatin Kano ta bayyana sarkin da ta amince yayi hawan Sallah a Kano

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *