
Rahotanni sun bayyana cewa hukumomi na shirin mayar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai jihar Kaduna dan ci gaba da tsareshi a can.
Hakan na zuwane yayin da ake shirin fara shari’ar sa akan wasu sabbin zarge-zargen da ake masa.
Hakan ya fito ne daga Sahara Reporters inda tace ta samu rahoton daga majiya me karfi.
Saidai bata bayyana sabbin zarge-zargen da akewa El-Rufai ba.
Majalisar jihar ta Kaduna dai ta bayyana yin bincike da gano aikata ba daidai ba a zamanin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na Gwamnan Kaduna.
A yanzu dai malam Nasiru Ahmad El-Rufai na tsarene a hannun Hukumar ICPC.