Friday, March 6
Shadow

Da Duminsa:Hukumar zabe me zaman kanta INEC ta sanar da ranar da za’a yi zaben shugaban kasa na shekarar 2027

Hukumar zabe me zaman kanta INEC ta sanar da ranar 20 ga watan Fabrairu na shekarar 2027 a matsayin ranar da za’a gudanar da zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Shugaban Hukumar zaben, Professor Joash Amupitan ne ya bayyana haka ga manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Yace zaben shugaban kasa dana ‘yan majalisun tarayya za’a yishi ne ranar 20 ga watan Fabrairu inda kuma zaben Gwamnoni dana ‘yan majalisar jihohi za’a yishi ne ranar 6 ga watan Maris.

Ya bayyana cewa, sun shirya tsaf dan gudanar da zaben.

Karanta Wannan  Ra'ayinane ba tsoron EFCC ba yasa na koma APC, kuma idan dai ana son Najeriya ta dore a matsayin dunkulalliyar kasa sai an zabi Tinubu a 2027>>Okowa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *