Friday, December 5
Shadow

Da Duminsa:Kotu ta kwace kujerar dan majalisar wakilai daga jihar Zamfara bayan da ya fice daga jam’iyyar PDP zuwa APC

Babbar Kotun tarayya dake Abuja ta kwace kujerar dan majalisar wakilai, Abubakar Gummi bayan da ya bar jam’iyyar PDP zuwa APC

Abubakar Gummina wakiltar mazabun Gummi/Bukkuyum ne a majalisar wakilai ta tarayya.

Mai shari’a, Obiora Egwuatu ne ya yanke wannan hukunci inda yace kada kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas ya sake kallon Abubakar Gummi a matsayin dan majalisar.

Hakanan alkalin ya kuma baiwa hukumar zabe me zaman kanta INEC umarnin sake shirya wani zabe dan cike gurbin dan majalisar nan da kwanaki 30.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon yanda Gwamnan Jihar Edo ya shiga cikin Kwalbati yana duba aiki da ya dauki hankula

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *