Monday, March 24
Shadow

Dala Dubu $5 da aka bamu bana cin hanci dan mu goyi bayan Shugaba Tinubu ya cire gwamnan Jihar Rivers bane, Barka da Sallah ce aka bamu>>Inji ‘Yan majalisar Tarayya

Dan majalisar Tarayya wanda shine shugaban kwamitin dake kula da babban birnin tarayya, Abuja, Mukhtar Aliyu Betara ya bayyana cewa, tabbas an raba musu dala $5000 da ake ta rade-radi.

Saidai yace ba kamar yanda ake yadawa ba wai cin hanci ne aka basu dan su amince da tsige gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara bane.

Yace an basu kudin e a matsayin barka da sallah wanda kuma dama an saba duk shekarar ana basu.

Dan jarida, Jafar-Jafar ne ya bayyana haka inda yace yayi magana da dan majalisar.

Karanta Wannan  HOTUNA: Masoyan Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi ll sun ɓarke da murna bayan da Kotun ɗaukaka ƙara ta yanke hukunci kan dambarwar masarauta a yau Juma'a a Abuja

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *