Tuesday, May 19
Shadow

Dala Dubu $5 da aka bamu bana cin hanci dan mu goyi bayan Shugaba Tinubu ya cire gwamnan Jihar Rivers bane, Barka da Sallah ce aka bamu>>Inji ‘Yan majalisar Tarayya

Dan majalisar Tarayya wanda shine shugaban kwamitin dake kula da babban birnin tarayya, Abuja, Mukhtar Aliyu Betara ya bayyana cewa, tabbas an raba musu dala $5000 da ake ta rade-radi.

Saidai yace ba kamar yanda ake yadawa ba wai cin hanci ne aka basu dan su amince da tsige gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara bane.

Yace an basu kudin e a matsayin barka da sallah wanda kuma dama an saba duk shekarar ana basu.

Dan jarida, Jafar-Jafar ne ya bayyana haka inda yace yayi magana da dan majalisar.

Karanta Wannan  Kalli yanda Wani Bayerabe yayi tsalle ya fada Rijiya bayan da ya sha kwaya ranar Sallah Saboda murna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *