Saturday, December 13
Shadow

Dalibar jami’ar Federal Polytechnic Bida, Jihar Naija me suna A’isha ta mutu a dakin Saurayinta me suna Akin wanda shima an sameshi ba rai

An samu dalibai biyu na jami’ar Federal Polytechnic  Bida, dake jihar Naija wanda masoya ne sun mutu a daki daya.

Dalibar me suna A’isha ta mutu ne a dakin saurayinta me suna Akin wanda shima an iskeshi ya mutu.

Kafar Sahara Reporters data ruwaito labarin tace an samesu duka bakunansu da kumfa wanda ake kyautata zaton guba ce suka sha suka mutu.

Saidai zuwa yanzu babu wani karin bayani kan lamarin amma ‘yansanda sun dauki gawarwakin zuwa mutuware.

Hukumar makarantar tasu ma taki tace uffan kan lamarin.

Karanta Wannan  Sadiya Haruna Ta Grime Ni, Shekaru Na 35 Ita Kuma Shekarunta 48, Kuma Kafin Mu Rabu Na Ba Ta Hakuri Ya Fi Sau Milyan Duk Da Cewa Ita Ta Yi Min Laifi, Saboda Na Kama Ta Tana Cin Abinci Da Wani Gardi Da Muharraminta Ba, Cewar G-Fresh Al'Amin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *