Thursday, February 5
Shadow

Dan kudu zamu tsaida takarar shugaban kasa a 2027>>Inji Jam’iyyar PDP

Jam’iyyar PDP ta sanar da cewa, dan kudu zata tsayar takarar shugaban kasa a shekarar 2027.

Jam’iyyar ta bayyana hakane a zaman masu ruwa da tsaki da ya wakana a jiya.

Sannan ta canja wajan da zata gudanar da taronta na zaben shuwagabannin jam’iyyar wanda a da za’a yi a Kano, yanzu a jihar Oyo za’a yi.

Ana zargin an yi hakanne dan shiryawa gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinda hanya a shirinsa na tsayawa takarar shugaban kasa a 2027.

Saidai hakan kuma zai zama koma baya ga Nyesom Wike wanda tuni dangantaka tsakaninsa da Gwamna Makinde ta yi tsami.

Karanta Wannan  Majalisar Jihar Kano ta mayar da Yaren Hausa a matsayin wanda za'a rika amfani dashi wajan koyar da dalibai a makarantun Firamare da karamar Sakandare

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *