Friday, July 17
Shadow

DSS ta maka Sowore da X da Facebook a kotu saboda ya kira shugaba Tinubu me laifi kuma ya zargi shugaban kasar da fadar ba daidai ba game da magance matsalar rashawa da cin hanci a Najeriya

Hukumar ‘yansandan farin kaya ta DSS ta maka mawallafin jaridar Sahara reporters, Omoyele Sowore a kotu bisa zarginsa da kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu me laifi.

Sannan an zargi Sowore da kuma bayyana shugaban kasar a matsayin makaryaci saboda yace yayi ikirarin magance matsalar rashawa da cin hanci a kasar Brazil amma Sowore yace maganar ba gaskiya bace.

Sowore ya wallafa cewa DSS na shirin kaishi kotu kuma a shirye yake idan an kaishi Kotun ya ansa gayyata.

Karanta Wannan  Hotuna: Yadda dan gidan ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya kammala digiri na biyu a Jami'ar kasar Ingila, Inda ya karanci fannin shari'a. Ministan ne ya wallafa hakan a shafinsa na X, inda yake alfahari da hakan

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *