
Babban malamin Addinin Islama, Sheikh Salihu Zaria ya baiwa mutane shawarar su daina nuna ragowa.
Ya bayyana hakane a wani faifan Bidiyonsa da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka jishi yana cewa duk wanda ya zageka ka rama.
Wasu dai sun ji dadin wannan wa’azi amma wasu na ganin kamar kan malam ya dau zafi ne a yayin wannan magana.
Malam dai kan yi wa’azi da kan dauki hankulan mutane sosai a kafafen sadarwa.