
Sanata me wakiltar mazabar ogun West ya bayyana cewa jihar Ogun na daf da shiga sahun jihohin da ake hako danyen Man fetur a Najeriya.
Yace shiri yayi nisa wajan fara hako man fetur a tsibirin Tongeji dake karamar hukumar Ipokia a jihar.
Yayi bayanin ne a Ota wajan wani taro inda yace wajen na tsakanin Najeriya ne da kasar Benin Republic.
Yace an samu wannan dama ne saboda kokarin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na karfafa tattalin arzikin Najeriya.