
Shugaban jam’iyyar APC, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayar da tabbacin cewa, Gwamnoni da yawa zasu sake komawa jam’iyyar.
Ya bayyana hakane a wajan taron karbar gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori da ya koma jam’iyyar ta APC.
Ganduje ya jinjinawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu saboda shugabanci na gari da yake samarwa a Najeriya.
Ganduje yace a yanzu suna da gwamnoni 22 kenan a jam’iyyar APC inda yace mutane su saka ido su gani akwai karin gwamnonin da zasu dawo APC nan gaba.