Wednesday, April 15
Shadow

Gyare-Gyaren da muka yi akwai wahala, amma suna bada sakamako me kyau>>Inji Gwamnatin Tarayya

Gwamnan babban Bankin Najeriya, Cardoso ya bayyana cewa, Gyare-Gyaren da gwamnatin tarayya ta zo dasu babu sauki amma suna bayar da sakamako me kyau.

Ya bayyana hakane a wajan taron da aka gudanar a birnin Washington DC na kasar Amurka wanda IMF da bankin Duniya suka shirya.

Yace wadannan Gyare-Gyaren sun dora Najeriya a turbar ci gaba kuma a yanzu suna bayar da sakamako me kyau.

Wasu daga cikin Gyare-Gyaren da gwamnatin tarayya ta kawo sune cire tallafin man fetur, cire tallafin dala da sauransu.

Karanta Wannan  Shekara biyu na yi ina wa Tinubu aiki a matsayin me magana da yawunsa amma bamu taba zama ni dashi ba ko sau daya>>Inji Aliyu Audu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *