Tuesday, November 18
Shadow

HASBUNALLAHU WA NI’IMAL WAKIL: Bèĺlò Țùŕjì Ya Kori Mutàñèn Gàriñ Bafàrawa

HASBUNALLAHU WA NI’IMAL WAKIL: Bèĺlò Țùŕjì Ya Kori Mutàñèn Gàriñ Bafàrawa.

Daga Datti Assalafiý

Shugaban barayin daji Be||0 Turj! ya kori mutanen dake zama a garin Bafarawa, kusan gaba daya mutanen garin sun watse zuwa neman mafaka a halin da ake ciki

Sannan Be||0 Turj! ya aika takarda zuwa ga mutanen garuruwan Kamarawa, Arume da Kagara, ya ce baya son ganin wani mutum a cikin garuruwan daga yau Lahadi zuwa misalin karfe 4 na yammaci

Akwai labarin da na gani, ance a daren jiya kadai kusan garuruwa 5 barayin daji suka yiwa hari a tsakanin jihar Katsina da Zamfara

Sannan jiya ‘yan bindiga sun kai harin ta’addanci makarantar Sakandare (GSS) dake garin Raka a karamar hukumar Tsafe jihar Zamfara inda suka kashe Malami sannan sukayi garkuwa da mutane da yawa

Karanta Wannan  Amarya ta zuba Gguba a Abincin walimar aurenta a jihar Jigawa, Mutum daya ya mutu, Ango ya kwanta rashin lafiya

Abubuwan da suke faruwa a yankin Arewa na matsalar tsaro kamar babu Gwamnati a Nigeria, shin menene manufar da ta sa a yanzu Be||o Turj! yake ta tashin mutane da garuruwansu?

Ana ta zargin cewa duk garin da aka tasa a yankunan da ake fama da matsalar nan to akwai ma’adinan karkashin kasa masu daraja a garin, idan aka tada mutanen gari watakila Kasar Faransa zata mamaye gurin ta cigaba da mining kenan???

Kuma idan kun lura, ba’a so a kawar da Be||o Turj! ne, domin ba shakka akwai manyan azzalumai maciya amana da suke amfana da ta’addancinsa

Mu hadu mu kai karansu gurin Allah, duk wanda yake da hannu a wannan matsala Allah Ka dauki rayuwarsa

Karanta Wannan  An kama mutane 2 da yiwa yarinya me shekaru 12 fyàd a jihar Yobe

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *