Thursday, March 26
Shadow

Hezbollah ta ce ta harba makaman roka zuwa kudancin Isra’ila

Hezbollah ta harba gomman rokoki zuwa kudancin Isra’ila, a cewar ƙungiyar a wata sanarwa.

Ta ce ta far wa shingayen sojoji da kuma wuraren ajiye makamai ta hanyar amfani da makamai masu linzami,a wani matsayin martani ga hare-haren da Isra’ilar ta kai kudancin ƙasar.

A wata sanarwa ta daban, dakarun tsaron Isra’ila (IDF), sun ce an harba rokoki aƙalla 35 daga Lebanon kuma hakan ya shafi shingayensu.

An jikkata wani mutum mai shekara 50 a yankin Galilee, a cewar sojoji Isra’ila.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojin saman ƙasar sun kakkaɓo rokoki da dama da Hezbollah ɗin ta harba yayin da wasu kuma suka yi lahani a wasu yankuna kusa da garin Ami’ad.

Karanta Wannan  Kalli Hadiza Gabon ta wallafa hotunan ta lokacin tana 'yar Lukuta da yanzu data rame inda tace kula da jiki na da muhimmanci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *