Friday, January 2
Shadow

Hotunan Mahajjata da aka kama sun yi safarar Kwa-ya zuwa kasa me tsarki

Hukumar yaki da sha da safarar miyagun kwayoyi ta NDLEA ta kama wasu mahajjata a otal din Emerald Hotel dake Ladipo a jihar Legas suna hadiye hodar Iblis da zasu tafi da ita kasa me tsarki.

An kamasu ne ranar Laraba, 5 ga watan Yuni kamin tashin jirgin su zuwa kasa me tsarkin.

Kakakin hukumar, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar inda yace wadanda aka kamadin, Usman Kamorudeen na da shekaru 31, sai kuma Olasunkanmi Owolabi me shekaru 46, akwai kuma Fatai Yekini me shekaru 38, sai Ayinla Kemi.me shekaru 34.

Yace an kwace dauri 200 na hodar Iblis din daga hannun wadanda ake zargi.

Karanta Wannan  Mugunta ko cin Amana? Ji yanda shugaban wani kauye a jihar Katsina ya karbi cin hancin Naira dubu dari bakwai(700,000) ya amince aka kaiwa mutanen kauyensa hari har aka kash-she 30

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *