
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC, Peter Obi ya bayyana cewa, idan ya zama shugaban kasa, daga Kaduna zai rika gudanar da mulkinsa.
Ya bayyana hakane a wajan wani taro a jihar Kaduna da ya halarta.
Yace Kaduna ta yi kusa da Abuja sosai ta yanda idan ta kama shugaban kasa zai iya zuwa ya gudanar da taro a Kaduna har ya huta ya kuma koma Abuja.
Yace idan ya zama shugaban kasa, zasu dawowa da Kaduna kwarjininta data rasa.