Thursday, March 5
Shadow

Ina sane da ana shan wahala a Najeriya amma ba laifina bane>>Tinubu

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince da cewa ya yadda ana shan wahala a Najeriya.

Tinubu ya bayyana hakane a ganawar da yayi da tsaffin shuwagabannin majalisar tarayya wanda Ken Nnamani ya jagoranta.

Ya bayyana cewa sakacin gwamnatocin da suka gabata ne ya jefa kasar a halin da take ciki.

Yace amma da hadin kai da aiki tare za’a samu ci gaba a Najeriya.

Tun bayan da shuyaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ya cire tallafin man fetur ne dai Najeriya ta shiga cikin halin matsin tattalin arziki wanda har yanzu bata fita ba.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyon wani matashi daga jihar Katsina na fadin cewa, bai taba samun farin ciki irin na gwamnatin Tinubu ba, Yace da mata daya gareshi yanzu ya kara, hakanan kasuwarsa ta habaka kuma matsalar 'yan Bìndìgà ta gushe a karamar hukumarsa ta Jibia

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *